DOGUWAR HANYA CHAPTER 11

Advertisements

_____

Menene yanzu yake damunta?” General ya wurgawa Cyama wannan tambayar acikin waya

“Batacin abinci jininnkuma har yanxu be sauka ba inji Dr.” Nisawa yae yace

“Kibata wayar tam zan mata magana ne” mik’a mata tae tace

“Mom, dad ne ze miki magana” karb’a tae ta kara a kunnen ta

Advertisements

_____

“Adaman General ya jikin ki?” Murmushi tae jin abinda yace

“Naji sauk’i Daddyn Twins” ta fad’a tana me k’ok’arin nuna masa bata cikin wani ciwo

“Na samo miki yaranki, ki gayawa jinin nan ya sauka da sauri, ga Abu sufyan ma ze miki magana” Da sauri ta tashi zaune tana dafe kanta

“Da gaske kake?”  Amaimakon taji muryan General setaji muryan Abu sufyan

“Mom sannu da jiki ya jikinki?” Mayar da numfarfashi tasomayi sauri da sauri kantace cikeda farin ciki

“Sannu Sufyan, ina kuka shiga haka kuka nemi d’agamun hankali mahaifiyar Dawood ma tashiga damuwa me tsanani” murmushi yae

“Mom ki kula da kanki kawai da lafiyanki mufa muna nan lafiya lau, wayoyin mune kurun aka sace mana duka, amma dukanmu muna cikin qoshin lafiyax harma tare da dad zamu dawo, please kiji sauqi kinji?” Ya k’arashe maganar cikin shagwab’a, tabbas ko wannan halin ya isa ya nuna cewan Abu sufyan d’intane, murna awurinta ba’a magana haka sukaita hira daga bisani sukai sallama bayan ya sanar mata Hurairah yana wanka gudun karta gano bashida lafiyane.

***********

   Shirinsa tsaf yae shida Dad da dawood sannan aka kwashesu zuwa airport dan da jirgi zasu koma abuja, tafiyar dabata wuce 40 mns ba ta sadasu da Abujan, Rahama wacce basu tab’a shiga acikintaba suka tsinc8 kansu aciki ganinsu a babban birnin tarayya, da wheelchair aka d’auki Abu Huraira, su Lawuri se zare ido suke, dama haka duniyar take da ababen kallo iri iri, kalli motoci kaman ba gobe dama haka rayuwar take suke cikin mugun jejin cen basu masan abinda ake ciki ba, kodai wai mafarki ne takeyi? Kokuma shin aa Aljanaine suka sato ta? Tama rasa me zatai tunani akai a haka har aka umarcesu da shiga motar suka d’unguma dukkansu zuwa gida.

************

     Abu Huraira kam asibiti aka wuce dashi inda suka k’ara duba k’afar alhamdulillah aiki yayi kyau, sedai fatan samun lafiya, Abu sufyan kuwa shida sauran dukansu gida suka wuce, kai tsaye d’akin su ya wuce ya shiga toilet yafi 2 hours yana dirxar jikinsa, yasha mamakin yanda gashi ya masa yawa sekace wanda ya shekara baya cikin al’umma, koda gake ba abin mamaki bane tunda yaga yanda gaba d’aya Abu Huraira yazama sekace wani tsohon zaki jikinsa duk gashi, bashida nutsuwar daze wani b’ata lokacin gun kwalliya dukda haka  ya shirya tsafi acikin k’ananun kayan sa shirt blue da wando fari qal, hannunsa ya wurgawa kallo bemasan dunuyar da agogon sa ya shiga ba kuma dashine ake ganeshi, zoben dai yana nan, murmushi yae ya fito daga d’akin nasa bayan ya feshe jikinsa da turaruka masu tashin k’amshi me sanyi da sanyaya zuciya.

A k’asa yaci karo da Hanifer bayan daya sakko, zuwa tae tana masa murmushi yabkalleta cikeda kulawa

“Hanny Baby, kina lafiya?”

“Ka rikitar dani yaa Sufyan nasan kaine ma, gashinan kanamun wannan kallon” murmushi yae

“Naji nine ya akayi?”

“Duk ka canja fa, kwata kwata kaman  ba kaiba” gemun daya masa tsawo ya shafa yana murmushi bece komai ba

“Yaa Huraira fa?”

Kallonta yake har yanzu

“Huraira zazzab’i yake yana asibiti ma, daga zaran nayi aski gunshi zanje, ku da dare sekuje yanzu wannan bak’in ki nuna musu sui wanka ki basu abinci da lemo me sanyi sannan ki wadata su da suturu wannan kayan jikinsu ai destroying nasu ki baiwa gate man ya qonasu” Jikinta duk yae sanyi

“Yaa Sufan kace ina gayar da yaya huraira plss” Ta qarashe maganar wane zatai kuka jinjina kanshi yae ya juya kawai.

Kai tsaye shagon aski yaje yae askin san sannan ya wuce gun mom, murna awurinta ba’a ma magana, bayan sun gama gaisawa take tambayar sa Huraira yace ciki  zolaya

“Lallai mom inaji dake, toba zagwad’in ganinki ya sanya gaba d’aya na manta ban sanar dake ba, kinsa halin Brother zazzab’i ya kamashi fa  yanzu haka yana kwance agidan amma yace a gaisheki, idan naje gida zan kira kui magana  danki tabbatar yana lafiya, yamaso yazo nace kasan Mom bazataji dad’i ba idan har ta ganka  kana layi kuma kazo dubata” Murmushi tae

“Allah ya bashi lafiya, waime ya faru dakune Kyautar Allah nashiga damuwa fiyeda tunaninka, sekuma naganka fes fes amma karame sosai fa” kallon ta yae cikin murmushi

“Mom ya bazan rame ba bayan banida abinda zanci, kin sani nifa idan bake kika girka abuba ko Baba ladi bana iya cinshi, shisa nayita shan yoghurt kawai harna rame” ya k’arashe maganar cikin tsananin shagwab’a har yana d’aura kanshi asaman kafad’arta, hannu ta sanya ta tureshi da wasa, tana dariyabta kally Cyama

“Cya zanga ranar da yayanki ze girma, kalli shifa gotai gotai dashi yake so ya k’arasa ‘yar tsohuwa” murmushi Cyama tae

“To mom tun yaushe rabon daya ganki mom? Ni yaa Sufyan kurun ka hau cinyar tama” Dariya sukai dukkansu sannan suka shiga hirar duniya, anan yaci abinci sosai sannan yace zeje gida, bayan nan gun Huraira ya wuce, suka zauna sukaita hira yake gaya masa yanda yae da mom, qaramar wayar daya siya ya zaro ya kira mom ya baiwa Huraira jin yana lafiya ba qaramar nutsuwar ya saukar mata ba, take cewa base yazo ba ya zauna abinshi seyaji sauqi.

*************

   Su Lawuri agun wanka ma ansha fama dasu dankuwa Hanifer har mamakin wannan gidadancin take, to suwaye ga basajin Hausa, se Sighn language (yaren kurame) suke amfani  dashi, da k’yar ta tsaya sukai wanka ta basu dogwayen riguna na material nanma tasha fama seda ta saka musu kuma sesuka kasance a takure dan basu saba ba, abinda ma takula dashi shine basa jin dad’in kayan, abinci kuwa ansha  fama dasu, shinkafa da miyane amma ko yanda zasuci basu sani ba, gaba d’aya kan Hanifer ya d’aure seda ta zauna ta ebo nata tanaci suna gani sannan suka ci, bazasuce basuji dad’i ba amma dai basu sababa kam, hakan datakula basu maci da yawa ba ya sanya ta kawo musu ‘ya’yan itatuwa  ba laifi sukam sunsha sosai, bayan nan kuma d’aki ta kaisu suka kwanta sabida rage gajiya, ita baiwar komai d’ari d’ari takeyin sa, danko gadon kasa kwanciya tae kusa da uwar gijiyar tata se a qasabta kwanta babu wanda ga mayar da tsawon 30mns acikinsu batare da yayi bacci ba.

********

  Sufyan kuwa bayan nan Gidansu Ayusher ya wuce, a waya yae kiranta tafito tana tafiya cikeda yanga ta d’aukar hankali, sanye ajikinta farar doguwar jallabiya ce da mayafinta ja, agaban rigar ko ina an rubuta Ayusher da manyan haruffa da jajayen duwatsu, agogon hannunta ma fari ne qal, shima jikin fatar rad’am zaka hango an rubuta masa Ayusher da jajayen duwatsu takalmin k’afarta jane gaba d’aya, ta zuba asalin kyau dan har  bayan rigar ta Ayusher ne zane da red stones, tana tafiya tana taunar cingom, se wani murmushibtake fesa masa yayinda ya kawar da kanshi gefe d’aya azuciyar sa yana jin haushin halayen Ayusher, bud’e mab’allin motar  tae  tashiga gefen me zaman banza ta zauna, k’amshin turarukansu suka daki hancin juna kowannen su seda ya lumshe idan sa, watsa masa kallo tae

“Yau da kanka a gidanmu pure heart?” Gajeran tsaki yaja cikin takaici

“Kewai when zakiyi hankali ne?, kinzo mun ba sallama kin shigo ba gaisuwa kin soma zuba surutu akaina” Sadda kanta tae, mantawa take dawa yake gabanta ta manta masifar shi

“Am so sorry , Assalamu Alaika kuma ina wuni?”  

“Alaikissalam, sorry dama kud’in nan na kawo miki sauri nake da inda zani” cikin mamaki ta kallesa

“Wane kud’in kuma pure heart?” Murmushi yae

“Look Ayusher banzo nan mui wasa ba, kud’in dakika turamun nagode sosai, shine na dawo dashi” a yamutse ta kalleshi cikin hargitsi

“Haba Father sword mesa ni kome zan maka arayuwa bazan burgeka bane ba? Kud’in kaman banida shi zakace zaka dawomun dashi?” B’ata fuska ya k’arayi

“Nasan kinadashi shisa nace ki bani aro ai, Ayusher plss karki b’atan lokaci, nagode sosai da kulawa da kuma taimako, so ki karb’a kud’in nan” Jikinta yae sanyi inda sabo tasan halin Sufyan kozata mutu tunda beso karb’a ba baze karb’a ba, cikin takaici ta karb’a tace

“Thank u” murnushi ya sake mata

“Zan kiraki anjima idan na nutsu, karki kirani dan Allah da kaina zan kiraki” kallonsa tae yanxu kam  har k’walla ya taru a idanta

“Amma sufyan kasan yanda mutane ke sona, kasan yawan samarin dake tururuwa akaina kaine kad’ai kake wulaqanta ni, yanzu meye laifi idan ni na kiraka fisabilillah” abinda yake had’ashi da ita kenan

“Kin iya  jinjina yawan masoyanki, kinga Ayusher dan Allah jeki” Cikin fusata tabar cikin motar, tsaki yaja shikan yae gaba  da motarsa zuwa gida.

*********

  Abin duniya ya soma damun lawuri, tarasa inda zata tsoma ranta, baccin ma datayi da tulin mafarkai barkatai tayishi, dukda mahaifiyarta hankalinta ya koma gida, gida takeso taje taga me suke ciki amma batasan hanya ba, lallai seta koma gida bazata juri rashin mahaifiyarta ba, amma ko Wancen ze bita kuwa?.

Advertisements

_____

About Ismail

Check Also

WA GARI YA WAYA BY MARYAM IBRAHIM LATEE

Advertisements _____ : WA GARI YA WAYA Rubutawa MARYAM IBRAHIM LITEE (labarin zaman kishin mata …

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *