[Advertisements⬇️]

SALOON SO CHAPTER 15 - Bankinhausanovels
Mon. Mar 27th, 2023

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

SALOON SO CHAPTER 15

 

 

 

Jawahir ta shigo masa da kayan ciye ciye suka

shiga gaisawa. Faruk ya ce “Mutumin lallai naga

alamar ka warke har da tsarabar dan london ne ko jafan ko dan ijift ne ko America? Naga alamar

kamar jawahir tana da ciki ko?”

Haidar ya yi dariya ya ce “Ai ma ganinku nayi masu

tambaya yanxu kuwa kowa ya kalle ta yaga

shedar aiki ya yi kyau.

Suka kyalkyale da dariya tare da tafawa Faruk ya ce, “Bakinmu da nayi muku dai ya kama ku to Allah

ya raba lafiya, Ubangiji ta sa masu amfani ne ya

bamu masu albarka, don Hafsat tana can da nata

tsohon cikin.

Kai mutumin lallai kayu aiki, to Allah ya inganta

mana, Ubangiji ya raba su lafiya da shi. Bayan sun nutsu sun huta suka bude tsarabobi suka rinka bin

‘yan uwa da dangi suna rabo kowa aka bashi

tsaraba sai ya jinjina kudin da aka kashe masa.

Jikaken abu mai muhimmanci da tsaraba da mutum

sai yaga kamar shi suka yiwa tafiyar. Anty Maryam

ma da Uncle har gida suka zo yi wa su jawahir barka da kuma yi musu sannu da zuwa.

Da yake hutun su suka dakko zasu dade a nan a

gidan Ankul din suke zaune wanda ya zauna farkon

aurensa kafin aiki ya maida shi Abuja.

Jawahir ta

sha murna da ganin Antyna Maryam ta rungume ta suna ta dariya cikin jin dadi da walwala kamar sa

hadiye junansu.

Anty ki ce kin kusa haihuwa don naga cikin naki ya

yi tsini da yawa.”

Ta ce “Haka Ankul dinki yake cewa wannan cikin

ya fiye girma da yawa wai yana takura shi don na fiye langwai.

Jawahir tasa dariya ai gaskiya Anty sai yanzu na

gano sirrin da ya sa Ankul ya ke manne miki ko, na

ce ku ke manne wa juna, ashe haka rayuwar aure

take?

Hakika jawahir rayuwar aure aba ce mai dadi da nishadantarwa kwanciyar hankali da samun

nutsuwa. Amma fa duk wa ‘yannan abubuwan

basa samuwa sai ka yi da ce da abokin rayuwa

nagari.”

Haidar ya yi sallama ya shigo tare da cewa da

Maryam “Antynmu ai kin yi nauyi da yawa, da kin hakura da zuwan da sai muzo har gida mu gaishe

ku.”

Ta yi dariya tare da cewar ai bazan iya jure rashin

ganin diyata ba, yanda ake yi min zuzutun kara

kyan da tayi amma da nazo ai na gani idona ya

gane min kyakkyawar kulawar da ka yi ma ‘yata. Ya yi murmushi ya kalli jawahir ya ce, “Bebina zamu

fita da Ankul xuwa dare zamu dawo.” Ta

marairaice fuska kamar mai shirin kuka ya dafa ta

“Haba bebina mene ne kuma bana so ki bata ranki,

ba ga Antynki nan zata taya ki hira ba, sai mun

dawo zai dauke ta su ta fi. Ta yi murmushi yayin da ta juyo ta kalli Anty maryam. Ta ga ita ba ta saurari

su ma, hankalinta yana kan littafi tana karantawa.

Haidar ya riko ta suka yo falon tsakiya ya zauna a

kujera ya dorata kan cinyarsa “Meye damuwarki

babyna?

Ta yi rau rau da ido har sunkawo kwalla ta ce “Ni ba komai va ne ina tsoron kada Ankul ya sake

cewa ka dawo da Kausar ne, ba zan jure ganin

kana yi mata magana ba bare har ka shiga dakinta

ka kwana mun zama mu biyu da matsayi daya a

wajenka ta saki kuka.

Haidar ya rungume ta yana rarrashinta. “Kar ki damu Bebyna, daman can kaddara da

sha’awar kare kaina daga zina ita ta sani auren

Kausar, ki sa a ranki tsakanina dake mutu ka raba ne

takalmin kaza aurenmu auren zobe ne ba saki

ba yaji ba kishiya har avada.

Kuma na ji wai SULAIMAN BOMBOY za ta aura. Ta ce, “waye kuma SULAIMAN BOMBOY?” Ya ce wani yaro

ne dan karami amma ya nace wai shi a lallai sai ita.

Ta ce, “Um. Ta dako kai da sauri “Allah yayana?

Ya ce, “Sosai ma kuwa ta yi saurin kankame shi

tana sumbatarsa, cikin murna ya dako ta yana

dariya muje kada Ankul ya gaji da jira. Suka fito babban falo jawahir ta ce “Ankul ka bar

min Anty ta kwanar min anan.” Ankul ya girgiza kai

ya ce, jawahir kenan har yanzu

dai kina tare da kuruciya, to idan haihuwa tazo

kuma cikin dare ku yi yaya da ita, ku da kuke duk

farin shiga? Gaba daya suka sa dariya suka fice ita kuma ta

koma gun Anty maryam suka bude shafin hira. “Kin

gane ne Anty ni fa yanzu abun da nake tsoro

kada Haidar ya dawo da kausar don ban san yanda

zan yi ba, a da ban damu da aurenta sosai ba don

sannan ban damu da Yayan ba, amma anya yanzu yanda nake son Yaya Haidar muka shaku da shi

yake sona yana ririta ni yana tarairayata kamar kwai,

zan juri ganinshi da wata matar, wai! Naga

mace a rungume a kirjin Haidar, subhanallahi Allah

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

ma ya kiyaye, Anty ai wuka zan soka mata ta mutu

nan take. Maryam ta tuntsire da dariya ta ce “Allah ya kiyaye

jawahir,” Anty maryam ta ce “Ai na gaya miki wasu

matan su suke jawowa kansu ake yo musu kishiya,

na farko akwai matan da girman kai da ji da kai

tsabagen muskilanci ya yi musu yawa, to yawanci

masu irin wannan halin sai ki ga har mazajensu na aure su ke yiwa ko suna mantawa a karkashin

mazajen su suke? Dole mazan su ne gaba da su, dole

ne duk matsayinki da jin kanki, ki sauke su ki

yiwa mijinki biyayya ko dan ki samu tsira ma ranar

gobe kiyama, domin aljannar mace ta na tafin kafar

mijinta sai ya daga zaki shiga. Abu na biyu kuma shine, kazanta, sai ki ga mace awaje dagwas

dagwas da ita amma da zarar ta yi aure ta haihu sai

kiga ta zama kazama. Ba za ta tsaya ta tsabtace

kanta ba bare abincinsu ko abin shansu.

Wasu matan za ki ga kudin da aka ba su na cefane

a ciki zasu raga su boye baza su yo cefanan na duka ba bare su sarrafa girkin yanda zai yi dadi. Sai

mace tai abinci garau garau ba wadataccan kayan

miya bare mai kiji abinci kadas babu dadi abinci

babu kyau a fuska.

Bayan ta gama girkin ba ta san tai wanka ba ta

gyara jikinta, a’a sai ki ganta daga ita sai daurin kirji tana ta fama da kaurin wuta. Da kin doshi dakinta sai

zarnin fitsarin da warin dauda. Kin kai wa namiji

abinci ya yi cokali biyu ko uku ya ji ya kasa ci ya

ture saboda rashin dadi.

Baruwanki da kwantar da murya bare ki bincike

shi me ya hana shi cin abincin, a’a ke babu ruwanki sai ki ja kwanon gabanki ki kama ci ko ki kirawo

yaranki ki ce kuzo ku dau abinci babanku ya rage,

babu ruwanki da damuwarsa.

Idan dare ya yi kina kwance cikin yaranki kin saki

baki kina munshari kin bude nono kin saka wa

yaron da kike goyo a baki kin riga kin sabar masa, sai da nono a bakinsa zai yi bacci, da maigidanki ya

zo ya taba ki don ki taso yana da bukatarki ki kama

miya kina faman zumburar baki ke an takura miki

kin gaji, daren ma ba za’a barki ki huta ba, saboda

Allah mijin nan naki waliye ne da ba zai bukataci

mace ba in har Allah ya kare shi daga sharrin zina? Ai kuwa dole ya yi kokarin karo aure ko dan ya

samu me debe masa sha’awa.

Jawahir ta ce, “Yanzu Anty kina ganin wa’yannan

dalilai zasu taimaka wajen yo wa mace kishiya?

Anty maryam ta ce “Kwarai kuwa ai wadannan su

ne kan gaba, idan mace ta zamo bata daraja mijinta bata ganin mutuncin iyayensa tana wulakanta masa

‘yan uwa da abokanan arzikinsa to yana kara

aure gudun kada ta rusa masa zumunci da ‘yan

uwansa.

Jawahir ta ce, “To ai Anti in kika yi la’akari da wasu

mazan kwata kwata ba su san darajar mace ba, sun dauki mace baiwarsu abar korewa sha’awarsu, don

wani namijin zaki ga namiji yana wasa da

dariya a waje ki ga yana tayiwa ‘yan mata fara’a

yana jansu da wasa, amma da zarar ya shiga

gidansa sai ki ga ya koma kamar mala’ikan

mutuwa ya murtuke fuska babu alamar fara’a bare wasa, da ya ci karo da kwano ko wani abu nata

akan hanya zai bal da shi, kuma yana da rufin

asirinsa amma sai ya ba wa iyalansa dan kalilan din

kudin da ba za su wadaci girkin gidansa ba, ba

ruwansa bai damu da matsalar da suke ciki ba, bai

ja su a jikinsa ba, bare su saki jiki da shi har su dinga bayyana masa damuwarsu. Anty duk irin

wannan ai rashin adalci ne da sanin

darajar mace ko?

Anty maryam ta ce “Haka ne jawahir amma ni a

ganina idan Allah ya hada ka zama da irin

wa’yannan mazan to sai ka iya zama da su. Na farko mace ta dasa wa zuciyarta hakuri, ta zamo

mai juriya da tawakkali, na biyu ta kasance me

yawan ibada tai ta addu’a tana kai kukanta ga

Allah, na uku ta samu sana’a komai kankantarta

kada ta raina ta ta rike ta hannu biyu.

Na hudu ta zamo mai kyautata masa da yi masa biyayya ko dan ta samu tsira ranar lahira. Na biyar ta

kasance me tsafta da kwalliya da kasancewa

cikin kamshi. Na shida ta kasance cikin koyon iya

kissa da kwantar da kanta tana kaskantar da kanta

ko yaushe tana nuna masa shi ne sama da ita, na

bakwai ta kasance doluwa marar wayo ta zamo me kau da kai da duk wani abu da zai mata, na takwas

ta zamo mace me iya kula da rayuwarta wato tana

cin abubuwan da za su kara mata ni’ima a jikinta.

Na tara mace ta iya kwanciyar aure ta gano wace

irin kwanciyar aure mijinta ya fi bukata, me da me

da me mijinta ya fi sha’awa a jikin mace, sai ta rinka gyara nata yanda zai rinka daukar hankalinsa yana

bashi sha’awa ba tare da na mace daban ya burge

shi ba.

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

By Ismail

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

[Advertisements⬇️]