[Advertisements⬇️]

SALON SO CHAPTER 18 - Bankinhausanovels
Mon. Mar 27th, 2023

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

SALON SO CHAPTER 18

 

 

Bebyna ya za ayi na gaji da jin muryarki hasken

zuciyarta tare da jin lafiyarsu ita da bebyna.

Ta yi shashshekar dariya cikin kissa da jan hankali ta makale murya tare da lankwasar da murya ta yi

masa magana cikin yanga da marairaita.

“Honey na ka kwantar da hankalinka kalau muke

ni da bebynka, sai dai muna kewar dumin jikinka

na dan lokaci.”

“Okey, beby na kada ki damu karfe hudu zan dawo gida mu kasance tare zuwa wayewar gari ko beby

na?”

Ta ce “Um hum thank you Honey na, sai ka dawo

muna jiranka.

Ya sumbaci wayar ya huro mata isa ta cikin wayar,

ta shashshekar dariya da ta saukar wa da Haidar matsananciyar kasala yayi saurin ajiye wayar tare

da jan diguwar ajiyar zuciya.

Jawahir ta mike ta koma kicin ta debo fulas fulas

dinta ta malmala tuwon farar shinkafarta da ya

tuku ya yi luku luku da shi, kowanne ta malmala sai

ta sa alaida sannan ta jera acikin fulas din. Ta juyo hadaddiyar miyar wake da ganye wadda ta

dahu da hanta da koda da manja sai dan man kuli

kadan lallai jawahir kin iya hada abin da zai kara

muku jini da lafiya. Ta juye farfesun kifi irin ragon

ruwan nan ta zai zuba kamshi yake yi, ta bude

oben ta zaro gasashen naman ta da ya ji tumatir da albasa gashi yayi ruwa ruwa sai zuba kamshin

kayan kamshi yake yi. Ta hada lemon kwakwa da

madara sannan ta hada lemon abarba.

Kowanne ta zuba a jug ta cilla kankara ta rufe ta

kwashe kayan taje ta jere su a kasa yanda suke yi

yanzu saboda girman cikinta. Iya ce ta gyara mata kicin din da duk wajen da ya baci.

Jawahir ta shiga toilet ta tsalo wanka tare da tsala

kwalliya ta shafe shafe da hadaddun kamshi na

tururuka daban daban, simpil doguwar riga ta saka

me rubi biyu sai walwalin dutsunan jiki ne suke ta

zuba sheki. Ta dora sirrin mayafin akanta, ta futo falo ta zauna akan kafet ta mimmike kafafuwanta ta

wara su yayin da ta jawo rumote ta latsa TV ta

kama, ita kuma ta jingina da kujera tana kallo.

Haidar ya turo kofar tare da sallamar tasa, ya yi

saurin karasowa in da take ya zube a gabanta, ya

tarairayo ta jikinsa “beby na” ya shafa mararta ya ku ke ya beby na yana dawo na same ku beby na

komai lafiya ko?”

Cikin murmushi take daga kai tana amsa masa tare

da shafar sumarsa ta kansa.

“Sannu beby na zauna anan kada ki tashi na hau

sama na watso ruwa na zo mu fita muje mu ci abinci ko, ta daga kai.

Ya mike ya yi sama da sauri ya fada toilet be jima ba

ya fito ya shirya cikin kananan kayansa ya sakko,

ta mike ta taro shi ya rungume ta a barin damansa

“Muje restaurant mu ci abinci ko.?”

Ta langabe a jikinsa “Haba my love da raina da lafiyata na kasa yi maka girki har sai ka fita waje ka

ci? Honey na na yi mana girki.” Ya rike baki

“Bebyna bana hana ki wahalar da kanki ba? Daidai

sanda suka zauna gaban kayan abincin yana

bubbudawa, ta ce “Wallahi Honey na ba na son

naga ka ci girkin waje ko na wani wajen, shi yasa nake daurewa na yi maka da kaina.”

“San kyau bebyna, na gode Allah ya yi miki

albarka, ya raba ku da cikin nan lafiya”

Amin Honey na gode.”

Suna cin abinci Haidar yana zuba santi, jawahir tana

kyalkyala masa dariya. Da haka suka gama Haidar ne ya kwashe kayan, ya dawo ya same ta ta

kwanta kan kafet ya durkusa kanta yana yi mata

tausa sannu sannu yake matsa mata jikinta tare da

mulmula mata bayanta a hankali ta ke fadin “wash,

wash, tana limshe ido na son yin bacci.

Karar wayarsa ce ta sa ta bude ido, ya dauka “Hello Inna kina lafiya kwana biyu?”

Inna ta ce, “Lafiya lau nake ina jawahir din?”

“Ga ta kusa da ni.”

“Yauwa

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

daman dai kan maganar da nafara yi maka ne, zan

zo na taho da jawahir don ta yi wankan gida”. “Haidar ya katse ta da “Haba Inna saunawa zan

gaya miki ne ni matata babu inda zata duk girman

gidan nan bai ishe ta wanka ba sai kun dauke min

ita, wanne hali kuke son saka ni?’

Ta daka masa tsawa “Kai marar kunya bana son

shashanci, haihuwar farin zaka yi wa wauta yaushe zamu barta ko mu ma wayaye ne irin ka.? Ta kife

wayar tana mita.

Jawahir ta dora kanta akan cinyar Haidar tana

shafa fuskarsa. “Honey na me yake faruwa ne, don

Allah ka daina damun kanka.”

“Bebyna ba dole na damu kaina ba, suna kokarin raba ni da ke, bebyna wai za ki iya tafiya wankan

gida ki bar ni a nan har tsawon kwana arba’in da

‘yan kai?

Ta girgiza kai cikin yanayi na tausayi da son ta yi

kuka “Honeyna ba zan barka ba bazan yarda su

raba ni da kai ba, babu in da zan bi su.” Daidai lokacin da ta dafe cikinta tana wash, wash!,

yayi saurin rungumarta cikin rikita yana cewa,

“Bebyna menene, me ya faru da cikin nawa.?

My love bayana, cikina, kuguna, duk ciwo suke yi.”

Da sauri ya buga wa direbansa waya ya ce ya fito

da mota zasu asibiti. Ya dakko jawahir direban ya bude musu bayan mota suka shiga, ya rife ya ja

suka nufi asibitin, abinka da lafiyayyen asibiti tuni

suka shigar da ita dakinta daban ita kadai a ciki

Haidar ya furgice ganin yanda jawahir take wahala,

gani yake kamar ciro cikin ya dawo da shi jikinsa

shi ya yi nakudar ya haihu. “My love” ta kirawo shi maganarta kasa-kasa ya

durkusa kanta yana jinta “My love kayi waya su

Mama su zo kada na mutu basu ganni ba.

Ya sake rungume ta yana ta mulmula mata bayanta,

“Ki yi hakuri bebyna, ba za ki mutu ba kin kusan

haihuwa. Idan ki ka haihu sai na yi musu waya su taho da

kwarin gwiwarsu yanzu kuwa idan na gaya musu

hankalinsu tashi zai yi su zo su cika asibitin ai ta

damunki.

“Wayyo Honey.” Ta kankame shi tana nishi likitocin

da suke kanta suna gaya mata ta yo nishi suna danna mata cikin a hankali tana yo nishi jariri ya

fado tare da tsala kuka. Haidar ya yi saurin

daukansa a cikin jinin ya na ta murna.

Likitar ta yanke masa cibiya ta karbe shi ta mika wa

nas don su gyarashi

Wata sabuwar nakudar jawahir ta kama ba jumawa ta sunkuto ‘ya mace ba da jimawa ba wani da

namijin ya kuma futowa.

Ikon Allah, Allah mai baiwa, Allah mai kyauta, har

da kari jawahir ta haifi ‘yan uku maza biyu mace

daya, ‘ya’yan kyawawa kamar ‘ya’yan indiyawa

don kyau da ja, Haidar duk ya rikice don murna waya yake ta bugawa kawai baya tsayawa

gaisuwa sai dai ya basu labarin jawahir ta haifa

masa kyawawan ‘ya’ya har guda uku.

Kafin ki ce meye wannan, tuni asibitin ya cika ya

zama filin barka barka tare da murnar samun

wannan kyawawan karuwar da aka yi. Kwanansu daya a asibiti aka sallame su don ba sa

mun hutun suke ba saboda jama’a da suke ta

tuttudowa ganin wannan kyauta da Allah ya yi

musu da ba kowa ake ba wa ba.

Nan kuma gaddama ta kaccame in da Inna ta daga

gida za a yo da jawahir da jarirai shi kuma Haidar ya ce babu in da za ‘a kai masa mata da ‘ya ‘ya, sai da

Abbansa ya daka masa tsawa ya nuna masa bacin

ransa a zahiri sannan ya bari aka tafi da su jawahir

da yaran gidansu.

Shi kuma Haidar ya yi fushi ya yi nasa gidan ransa a

bace, yana shiga gidan yaga bakinsa yau ba jawahir a ciki can kuma ya rinka hango ta tare da

‘ya ‘yansa ‘yan uku, haba wa, tuni wani sabon farin

ciki ya sake mamaye shi ya shiga wanka ya sake

sabon wanka ya zira farae shaddarsa sabuwa kal

mai laushi sai sheki take yi kamar boyel.40

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

By Ismail

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

[Advertisements⬇️]