[Advertisements⬇️]

SALON SO CHAPTER 17 - Bankinhausanovels
Mon. Mar 27th, 2023

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

SALON SO CHAP 17

 

 

Subhanallahi! Lallai jawahir kin hada kyakkywan

lemo mai saurin saukar da ni’ima a jikin ta bar wa

iya rama ita kuma ta kara gyara falon da dakin megida ko ina ta turare shi da daddadan turaren

wuta na kamshi kowacce kusurwa ta feshe ta da

Air freeshner.

Ko ina ta sa ka AC sai sanyin dadi ne yake fita ta

gyara toilet ma shima ta turare shi da daddadan

kamshi, ta rufe sashinsa ta fito ta sakko ta shiga nata sashen ta sake gyarawa ta saki kamshi ta fada

toilet don yin wanka, ta dade tana murzar jikinta da

daddadan sabulu ga ruwan wankan nata ya sha

turaren wanka sai turarin kamshi ne yake tashi

Uku da rabi ta fito daga wanka ta dauro alwala ta

zo gaban mudubi ta fara tsara kwalliya shafa nan goge nan ko ina ya yi das, ta fara gabatar da sallar

la’asar, ta tsara kwalliya da wani pink din les mara

nauyi sai dai anyi masa shafi a ciki, duk da rigar fitet

ce ta dan fara kamata ko don cikin jikinta de da ya

fara bayyana, duk wata gaba ta jikinta ta mulke ta

da turaren kamshi, ta fesa na fesawa ta daura dan kwalin les din ya lafe kan gyaran gashin da ta yi.

Gaskiya ta yi kyau wannan da gasar sarauniyar

kyau zata je babu abin da zai hanata lashe gasar. Ta

dakko turare tana sake fesawa, daidai lokacin da

Haidar ya shigo da kyar yake daga kafa don

tsananin gajiya da yunwa tun break dan safe. Ya zube a kujerar falo yana mai nishi, “Bebina.”

“My love.” Jawahir ta fito daga cikin daki ta zagayo

gabansa idonsa yana limshe kamshin turarenta da

ya ji ne ya sa shi bude ido.

Subhanallahi, duk kyan jawahir sai yaga yau tafi

kullum kyau kamar wata fure aka dasa don kyau tuni gajiyar da ya kwaso ta ware, ya jawo ta

cinyarsa yana yi mata wani fitinannen kallo mai

tada sha’awa da raunannar zuciyar mai bege.

Ta sa hannunta ta rufe masa idon ya ciji hannun

nata ta yi saurin janyewa ta langabe kai cikin

shagwaba tana ‘yar kara tare da yarfe hannun nata.

Shikuwa Haidar tuni ya samu damar zira harshensa

a kyakkyawan bakinta, ya dade yana sumbarta ta

cikin shaukin so da igiyar bege da kyar ta zare

jikinta sakamakon wani nishi da ta ji yana yi gudun

ka da ta jawowa kanta jan gwam ta yi saurin haye wa samanta ta fada toilet dinsa ta hada masa ruwan

wanka, tana fitowa daga toilet din taga ya shigo

idon sa duk ya yi ja saboda fitina, ya sake jawo ta

ya mannata a jikinsa ya sake rungume ta ta

langabe cikin shagwaba take cewa, “My love ka je

ka y wankan kai muke jira fa Bebinka be ci abinci ba. Ya yi saurin cika ta ya dago kai yana shafa cikin

“Haba don Allah me yasa za ki bar min beby da

yunwa kina so ya galabaita ne, taho muje na fara

baki abincin tukuna, in kin koshi nayi wankan. Ta

make kafada ta ce um um ni dai ka shirya muje mu

ci tare. Ya jata ya zaunar da ita a gefen gado, to zauna nan yanzun nan zan fito ba zan dade ba.

Ya shige toilet din da sauri ita kuma ta tashi ta

dakko masa kayan da zai saka farar shirt ce da

bakin wando, ta feshe su da turare bai jima ba ya

fito daure da tawul sai wani akansa, ta yi saurin

tashi ta ciri tawul din kan nasa ta fara goge masa jikinsa, ta jashi gaban madubi ta shafe masa jikinsa,

da lafiyayyan cream me taushi da dadin kamshi, har

da shafa masa farar, hoda ta feshe shi da turare ta

ware masa kyansa ya karba ya saka.

“Au my love na manta ban sa maka man lebe ba”

ya sunkuyo da kansa ta shafa masa. “Inye! Nawan ba, ka kara kyau. Ya yi murmushi

tare da manna mata kiss a lebe ya riko ta suka taho

falo.kasa

suka sauko da kayan abincin ya hau kan kafet aka

baje don jawahir tafi sakewa.

Ta je firji ta tsiyayo hadadden lemon ta a je ya dau sanyi kuwa, ta zo ta ajiye ta dauki babban filet ta

bude fulas din ta sako musu sakwarar ta bude

miyar yayin da kamshinta ya bugi hancin Haidar ya

limshe ido yunwarsa ta dawo sabuwa, ta bude

daya filas din shima ta zubo musu hadin curaram

naman da ta soya da kwai, ta bude farantin hadin salak ta kalli Haidar ta ce, “My love bismillah.

Ya kalle ta yana murmushi sannu bebyna na gode

miki Allah ya saka miki da alheri Ubangiji ya yi miki

albarka, burinki kullum ki faranta min ki yi min abin

da zai sani farin ciki.

“To my love in ban yi maka ba wa zan yi wa, ina alfahari, ina matukar farin ciki da baiwar da Allah ya

yi min ta haduwa da gwarzon masoyi

Suka fara cin abinci dole jawahir ta rinka kyalkyala

dariya saboda yanda Haidar ya ta karkare yana ta

ziri tare da suba santi.

Komai sai da suka ci su ka koshi suka yi kat da su. Jawahir ta rinka tsiyaya wa Haidar hadin lemon

yana sha yana zuba santi shi dai ba don ya ji cikinsa

yana barazanar fashewa ba da ba zai bar sha haka

ba.

Jawahir ta kwashe kayan ta mayar kicin Haidar ya

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

jingina da kujera ya mimmike kafa ya dauki romote din tibi yana danne dannan tashoshi.

Jawahir ta dawo ta zauna ya juyo ya kalle ta cike da

kulawa yana murmushi ya ce, “Ya aka yi ne

bebyna? Ta jawo jikinta ta kwanta a cinyarsa cike

da sangarta, ya sa hannunsa kasan mararta yana

shafawa ya cire dankwalinta yana yaba kyan gashinta ya koma shafa kumatunta yana yaba

santsin fatarta da taushin jikinta kamar auduga.

Ya dora hannunsa kan kirjinta yana shafawa tare

da limshe ido jawahir ta ture hannunsa tare da

cewar “Meye haka kake yi a jikin ta tsitsiyar

kwaila.?” Ya yi saurin rufe mata baki da nasa ya dinga sumbatarta yana ruda mata jiki da wasanni

har sai da ya tabbatar ta manta da maganar

tukunna ya cikata.

Ikon Allah kenan duk yanda jawahir ta tsani

halayyar Haidar ba sa shiri da juna ba sa son

junansu, yau ga shi sun fi kowa kaunar junansu. Halayyar Haidar da jawahir ta tsana ta muskilanci da

kasaita da jan aji tare da rashin hayaniya ko

kwarniya yau tafi kowa murna da alfahari da

muskilancin Haidar da daukan kansa hade da

isarsa da kasaitarsa.

Tun da babu wata budurwa da ta isheshi kallo bare a kai gabatun magana har ya furta mata so, bata isa

ba kowacce.

So, kauna, aminci, yarda, shakuwa, duk ya tara su

ga tauraruwarsa jawahir. Bangaren Haidar kuwa

kullum sai ya yi wa iyayensa addu’a da fatan

gamawarsu da duniya lafiya saboda yanda suka hada shi aure da jawahir yanda da ya tsani

halayyarta ta miskilanci yau ga iyayi shagwaba.

Yanzu ga shi sun zamo abin alfaharinsa don suna

dada hura wutar kaunar jawahir a zuciyarsa.

Hakika ya yi sa’a da ace da samun kammalalliyar

mace ga kyau ga tsafta ga addini, ga usuli me kyau. Allah ya yi mata baiwa kala-kala na iya furta kalami

wanda lokaci daya zata siye zuciyar mai sauraronta.

Abu na biyu ta iya sahirtaccen kallo wanda zai jawo

afkawar mutum kogin begenta. Abu na uku ta iya

kissa da mutum ya so ta ko da baya ksunarta. Abu

na hudu yarinya ce me nutsuwa ga ta da ladabi da biyayya ga hakuri da tawakkali duk ta tara su.

Abu na biyar ta iya nau’ika na girki da abubuwan

sha ga ta da zakin hannu don duk wanda ya ci

girkin ta yai ta zuba santi da ya bawa kenan.

Abu na shida ta iya kwalliya gwanace wajen amfani

da hadaddun turaruka masu dadin kamshi, da san sutturar da ta dace ta saka kowanne yanayi da

kowanne lokaci.

Abu na

bakwai gwana ce wajen iya tsafta da gyaran gida

tun daga dakunnansu falukansu zuwa kicin

bandaki harabar gida ko’ina da launin turaren da take kamshinsa da yake yi

Abu na takwas ta riga ta gano makamar kama

Haidar domin ta fuskanci abin da ya fi so a jikinta

wata kirjinta, don haka koda yaushe ta kasance

cikin gyara kirjinta tare da sake kaya masu fito

mata da surar kirjinta. Abu na tara ta iya tarairayarsa tana ba shi

kyakkyawar kulawa ta siye zuciyarsa da

kyawawan halayenta, abu na goma na karshe

kuma, ta san sirrinkan kwanciya yanda duk yanda

ya juyata haka take binsa kowanne kokaci kuma

akwai sabon samfarin da zata gudanar masa a makwancinsa.

Ba ta gajiya da shi tana dauriya da jure bukatarsa

har sai ya gamsu don kanshi ba ta da korafi bare ta

nuna gajiyarta, ko ta ce ya fiye fitina

Wa’yannan halaye su ne suka ingiza kaunar

jawahir take dada ruruwa a zuciyar Haidar. Kwance tashi wajen Ubangiji babu wuya, ga shi

cikin jawahir ya shiga wata tara komai na haihuwa

sun tanada sai jiran haihuwar kawai suke yi.

Wata sabuwar sangarta jawahir take yiwa Haidar

saboda ganin yanda take bata tsantsar kulawa.

Cikin nata ya yi nauyi duk da haka ba ta yi sakaci da girkin megidan nata ba, bata sakaci duk yanda

Haidar ya kai da lallaminta da lallabata baya son

yaga tana wani aikin wahala don haka duk safiya

yake shiga kicin ya hada musu break.

Ya taimaka ma ta ta yi wanka shi yake yi mata

kwalliya, ya sa mata kayan da ya san baza su yi mata nauyi a jiki ba, ya rungumo ta zuwa falo kan

kafet ya zauna tana rungume a jikinsa yana bata

break a baki, sai daki ya kwantar da ita a gado

kamar wata jaririy yana yi mata tausa da matsa

sannu a hankali sai ya ga ta yi bacci sannan zai

shirya ya tafi office. Sha biyu na rana jawahir ta tashi daga bacci sannu

a hankali ta mike ta nufi kicin ta fara hada

abubuwan da zata dora girki, duk wani yanke

yanke da dake dake ko markade a bulanda me

take yi mata.

Ita kuma tana kula da girkinta da kuma hada lemummukan da ta san mijinta yafi so da sha’awar

shi.

Karfe biyu taje ta yi salan wayar Haidar ta sake

shigowa bugowarsa ta hudu kenan bayan tashinta

daga bacci.

Ta dauko “Hello Honey, na baka gajiya da yo waya ko”?

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

By Ismail

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

[Advertisements⬇️]