[Advertisements⬇️]
[Continue Reading⬇️]
SALON SO CHAP 17
Subhanallahi! Lallai jawahir kin hada kyakkywan
lemo mai saurin saukar da ni’ima a jikin ta bar wa
iya rama ita kuma ta kara gyara falon da dakin megida ko ina ta turare shi da daddadan turaren
wuta na kamshi kowacce kusurwa ta feshe ta da
Air freeshner.
Ko ina ta sa ka AC sai sanyin dadi ne yake fita ta
gyara toilet ma shima ta turare shi da daddadan
kamshi, ta rufe sashinsa ta fito ta sakko ta shiga nata sashen ta sake gyarawa ta saki kamshi ta fada
toilet don yin wanka, ta dade tana murzar jikinta da
daddadan sabulu ga ruwan wankan nata ya sha
turaren wanka sai turarin kamshi ne yake tashi
Uku da rabi ta fito daga wanka ta dauro alwala ta
zo gaban mudubi ta fara tsara kwalliya shafa nan goge nan ko ina ya yi das, ta fara gabatar da sallar
la’asar, ta tsara kwalliya da wani pink din les mara
nauyi sai dai anyi masa shafi a ciki, duk da rigar fitet
ce ta dan fara kamata ko don cikin jikinta de da ya
fara bayyana, duk wata gaba ta jikinta ta mulke ta
da turaren kamshi, ta fesa na fesawa ta daura dan kwalin les din ya lafe kan gyaran gashin da ta yi.
Gaskiya ta yi kyau wannan da gasar sarauniyar
kyau zata je babu abin da zai hanata lashe gasar. Ta
dakko turare tana sake fesawa, daidai lokacin da
Haidar ya shigo da kyar yake daga kafa don
tsananin gajiya da yunwa tun break dan safe. Ya zube a kujerar falo yana mai nishi, “Bebina.”
“My love.” Jawahir ta fito daga cikin daki ta zagayo
gabansa idonsa yana limshe kamshin turarenta da
ya ji ne ya sa shi bude ido.
Subhanallahi, duk kyan jawahir sai yaga yau tafi
kullum kyau kamar wata fure aka dasa don kyau tuni gajiyar da ya kwaso ta ware, ya jawo ta
cinyarsa yana yi mata wani fitinannen kallo mai
tada sha’awa da raunannar zuciyar mai bege.
Ta sa hannunta ta rufe masa idon ya ciji hannun
nata ta yi saurin janyewa ta langabe kai cikin
shagwaba tana ‘yar kara tare da yarfe hannun nata.
Shikuwa Haidar tuni ya samu damar zira harshensa
a kyakkyawan bakinta, ya dade yana sumbarta ta
cikin shaukin so da igiyar bege da kyar ta zare
jikinta sakamakon wani nishi da ta ji yana yi gudun
ka da ta jawowa kanta jan gwam ta yi saurin haye wa samanta ta fada toilet dinsa ta hada masa ruwan
wanka, tana fitowa daga toilet din taga ya shigo
idon sa duk ya yi ja saboda fitina, ya sake jawo ta
ya mannata a jikinsa ya sake rungume ta ta
langabe cikin shagwaba take cewa, “My love ka je
ka y wankan kai muke jira fa Bebinka be ci abinci ba. Ya yi saurin cika ta ya dago kai yana shafa cikin
“Haba don Allah me yasa za ki bar min beby da
yunwa kina so ya galabaita ne, taho muje na fara
baki abincin tukuna, in kin koshi nayi wankan. Ta
make kafada ta ce um um ni dai ka shirya muje mu
ci tare. Ya jata ya zaunar da ita a gefen gado, to zauna nan yanzun nan zan fito ba zan dade ba.
Ya shige toilet din da sauri ita kuma ta tashi ta
dakko masa kayan da zai saka farar shirt ce da
bakin wando, ta feshe su da turare bai jima ba ya
fito daure da tawul sai wani akansa, ta yi saurin
tashi ta ciri tawul din kan nasa ta fara goge masa jikinsa, ta jashi gaban madubi ta shafe masa jikinsa,
da lafiyayyan cream me taushi da dadin kamshi, har
da shafa masa farar, hoda ta feshe shi da turare ta
ware masa kyansa ya karba ya saka.
“Au my love na manta ban sa maka man lebe ba”
ya sunkuyo da kansa ta shafa masa. “Inye! Nawan ba, ka kara kyau. Ya yi murmushi
tare da manna mata kiss a lebe ya riko ta suka taho
falo.kasa
suka sauko da kayan abincin ya hau kan kafet aka
baje don jawahir tafi sakewa.
Ta je firji ta tsiyayo hadadden lemon ta a je ya dau sanyi kuwa, ta zo ta ajiye ta dauki babban filet ta
bude fulas din ta sako musu sakwarar ta bude
miyar yayin da kamshinta ya bugi hancin Haidar ya
limshe ido yunwarsa ta dawo sabuwa, ta bude
daya filas din shima ta zubo musu hadin curaram
naman da ta soya da kwai, ta bude farantin hadin salak ta kalli Haidar ta ce, “My love bismillah.
Ya kalle ta yana murmushi sannu bebyna na gode
miki Allah ya saka miki da alheri Ubangiji ya yi miki
albarka, burinki kullum ki faranta min ki yi min abin
da zai sani farin ciki.
“To my love in ban yi maka ba wa zan yi wa, ina alfahari, ina matukar farin ciki da baiwar da Allah ya
yi min ta haduwa da gwarzon masoyi
Suka fara cin abinci dole jawahir ta rinka kyalkyala
dariya saboda yanda Haidar ya ta karkare yana ta
ziri tare da suba santi.
Komai sai da suka ci su ka koshi suka yi kat da su. Jawahir ta rinka tsiyaya wa Haidar hadin lemon
yana sha yana zuba santi shi dai ba don ya ji cikinsa
yana barazanar fashewa ba da ba zai bar sha haka
ba.
Jawahir ta kwashe kayan ta mayar kicin Haidar ya
[Advertisements⬇️]
[Continue Reading⬇️]
jingina da kujera ya mimmike kafa ya dauki romote din tibi yana danne dannan tashoshi.
Jawahir ta dawo ta zauna ya juyo ya kalle ta cike da
kulawa yana murmushi ya ce, “Ya aka yi ne
bebyna? Ta jawo jikinta ta kwanta a cinyarsa cike
da sangarta, ya sa hannunsa kasan mararta yana
shafawa ya cire dankwalinta yana yaba kyan gashinta ya koma shafa kumatunta yana yaba
santsin fatarta da taushin jikinta kamar auduga.
Ya dora hannunsa kan kirjinta yana shafawa tare
da limshe ido jawahir ta ture hannunsa tare da
cewar “Meye haka kake yi a jikin ta tsitsiyar
kwaila.?” Ya yi saurin rufe mata baki da nasa ya dinga sumbatarta yana ruda mata jiki da wasanni
har sai da ya tabbatar ta manta da maganar
tukunna ya cikata.
Ikon Allah kenan duk yanda jawahir ta tsani
halayyar Haidar ba sa shiri da juna ba sa son
junansu, yau ga shi sun fi kowa kaunar junansu. Halayyar Haidar da jawahir ta tsana ta muskilanci da
kasaita da jan aji tare da rashin hayaniya ko
kwarniya yau tafi kowa murna da alfahari da
muskilancin Haidar da daukan kansa hade da
isarsa da kasaitarsa.
Tun da babu wata budurwa da ta isheshi kallo bare a kai gabatun magana har ya furta mata so, bata isa
ba kowacce.
So, kauna, aminci, yarda, shakuwa, duk ya tara su
ga tauraruwarsa jawahir. Bangaren Haidar kuwa
kullum sai ya yi wa iyayensa addu’a da fatan
gamawarsu da duniya lafiya saboda yanda suka hada shi aure da jawahir yanda da ya tsani
halayyarta ta miskilanci yau ga iyayi shagwaba.
Yanzu ga shi sun zamo abin alfaharinsa don suna
dada hura wutar kaunar jawahir a zuciyarsa.
Hakika ya yi sa’a da ace da samun kammalalliyar
mace ga kyau ga tsafta ga addini, ga usuli me kyau. Allah ya yi mata baiwa kala-kala na iya furta kalami
wanda lokaci daya zata siye zuciyar mai sauraronta.
Abu na biyu ta iya sahirtaccen kallo wanda zai jawo
afkawar mutum kogin begenta. Abu na uku ta iya
kissa da mutum ya so ta ko da baya ksunarta. Abu
na hudu yarinya ce me nutsuwa ga ta da ladabi da biyayya ga hakuri da tawakkali duk ta tara su.
Abu na biyar ta iya nau’ika na girki da abubuwan
sha ga ta da zakin hannu don duk wanda ya ci
girkin ta yai ta zuba santi da ya bawa kenan.
Abu na shida ta iya kwalliya gwanace wajen amfani
da hadaddun turaruka masu dadin kamshi, da san sutturar da ta dace ta saka kowanne yanayi da
kowanne lokaci.
Abu na
bakwai gwana ce wajen iya tsafta da gyaran gida
tun daga dakunnansu falukansu zuwa kicin
bandaki harabar gida ko’ina da launin turaren da take kamshinsa da yake yi
Abu na takwas ta riga ta gano makamar kama
Haidar domin ta fuskanci abin da ya fi so a jikinta
wata kirjinta, don haka koda yaushe ta kasance
cikin gyara kirjinta tare da sake kaya masu fito
mata da surar kirjinta. Abu na tara ta iya tarairayarsa tana ba shi
kyakkyawar kulawa ta siye zuciyarsa da
kyawawan halayenta, abu na goma na karshe
kuma, ta san sirrinkan kwanciya yanda duk yanda
ya juyata haka take binsa kowanne kokaci kuma
akwai sabon samfarin da zata gudanar masa a makwancinsa.
Ba ta gajiya da shi tana dauriya da jure bukatarsa
har sai ya gamsu don kanshi ba ta da korafi bare ta
nuna gajiyarta, ko ta ce ya fiye fitina
Wa’yannan halaye su ne suka ingiza kaunar
jawahir take dada ruruwa a zuciyar Haidar. Kwance tashi wajen Ubangiji babu wuya, ga shi
cikin jawahir ya shiga wata tara komai na haihuwa
sun tanada sai jiran haihuwar kawai suke yi.
Wata sabuwar sangarta jawahir take yiwa Haidar
saboda ganin yanda take bata tsantsar kulawa.
Cikin nata ya yi nauyi duk da haka ba ta yi sakaci da girkin megidan nata ba, bata sakaci duk yanda
Haidar ya kai da lallaminta da lallabata baya son
yaga tana wani aikin wahala don haka duk safiya
yake shiga kicin ya hada musu break.
Ya taimaka ma ta ta yi wanka shi yake yi mata
kwalliya, ya sa mata kayan da ya san baza su yi mata nauyi a jiki ba, ya rungumo ta zuwa falo kan
kafet ya zauna tana rungume a jikinsa yana bata
break a baki, sai daki ya kwantar da ita a gado
kamar wata jaririy yana yi mata tausa da matsa
sannu a hankali sai ya ga ta yi bacci sannan zai
shirya ya tafi office. Sha biyu na rana jawahir ta tashi daga bacci sannu
a hankali ta mike ta nufi kicin ta fara hada
abubuwan da zata dora girki, duk wani yanke
yanke da dake dake ko markade a bulanda me
take yi mata.
Ita kuma tana kula da girkinta da kuma hada lemummukan da ta san mijinta yafi so da sha’awar
shi.
Karfe biyu taje ta yi salan wayar Haidar ta sake
shigowa bugowarsa ta hudu kenan bayan tashinta
daga bacci.
Ta dauko “Hello Honey, na baka gajiya da yo waya ko”?
[Advertisements⬇️]
[Continue Reading⬇️]