[Advertisements⬇️]

SALON SO CHAPTER 16 - Bankinhausanovels
Mon. Mar 27th, 2023

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

SALON SO CHAPTER 16

 

 

Abubuwan da mace zata ci su kara mata ni’ima ba lallai sai ta fitar da kudinta

ta sai masu tsada ba, a’a daidai ruwa daidai tsaki, kada ki ce to ke ma ina kika

ga kudin bayan ba baki yake yi ba, ke ba wani abu da za ki siya don gyara

kanki.

To gaskiya wannan rashin wayo ne ai kan ki zaki gyara duk sanda namiji ya

kusance ki ya ji ki zam zam da ke, tsindum da ke dole ne ya rinka tattalinki ya

na baki kyakkyawan kulawa saboda yana son biyan bukatarsa. Amma ke baki

gyara kanki va, kin zauna gundin murhu duk wuta ta kone miki dan ruwan da

yake jikinki, mijinki ya zo ya ji kamas, saboda Allah me kike ganin zai faru?

Dole darajarki ta ragu idonsa, amma idan kika dage da shan su lemo, kankana,

rake, aya gwanda, ayaba, dabino, cukui, inibi, zogale, zaitun, tumatur, kwakwa,

zuma, nono, madara, gurji, dafaffiyar gyada, da sauransu duk irin wannan ba

karamin taimaka mana suke ba na kara mana ni’imar jikinmu.

Ko nera koma ki ka bayar a siyo miki dan kifi ki yi romonsa da kayan kanshi da

alvasa da tumatur kika watsa wake a ciki ya dahu luguf da dan alaiyahu ki yi

shi romo romo shi ma yana taimakawa, ki sami danyar gyada gwangwani daya,

aya gwangwani daya, waken suya gwangwani daya, alkama gwangwani daya, ki

hada ki jika a markado miki ki ta ce shi kamar gasara ki rinka damawa kina sa

madarar ruwa kina sha za ki ga yanda zai taimaka miki ya sakar miki da ni’ima

a jikinki.

Kinga abu mafi sauki idan kika sami ayarki kika jikata ta juku ki ka kai markade

kizo ki tace kayarki ki kara sikari ki rinka sha zata kara miki ni’ima sosai.

To kinga iri iren abubuwan nan idan mace tana yi zata taimaka wa kanta don

kare wulakancin namiji. To idan kuma ta iya gamsar dashi ta san sirrika na iya

kwanciya da da namiji to zata mallake shi a hannunta har a rinka zargin ta

asirce shi ne.

Jawahir ta ce, “To Anty me zai hana murubutanmu ba za su rinka wayar wa da

mutananenmu kai ba, ko dan sanin irin wannan sirrikan kwanciya don su ma su

mallaki mazajensu a hannu a daina yawan mutuwar aure? Maza su daina fita

bariki neman matan banza su rinka tsayawa iya matansu na sunna kawai?

“To ai jawahir matsalar da ake samu kin gane ne, marubutanmu suna iya bakin

kokarinsu na ganin cewar sun ganar da yawancin mutane yanda rayuwar jin

dadi ta aure take, to amma kash! Wani abu da ake kuka dashi wai sai ace suna

bata tarbiyar yara, wai yara kanana suna diban lattattafai suna karantawa, suna

ganin abin da bai kamata ba, wanda gaskiya ni kuma ina ganin ba haka ba ne,

domin idan kinga yarinya ta lalace to dama can lalatacciyarce iyaye suna ina

‘ya ‘yansu suke fita su shiga gidan amare su rufe kansu suna ganin kaset din

blue film ko America, ko ibo, ko fim din Turawa da yake bayyanar da tsiraici

karara da yanda ake nuna soyayya ta kazamar hanya. Wasu ma tare da samari

suke gani to meye ma ba zai faru ba wajan wannan kallon wa’yansu yaran

kuma da ake batawa ba su da wayewar kan ma da za su yi karatun littafin ake

jansu ayi musu fade, shi kenan hanyar lalacewarsu ta samu.

Wasu yaran kuma rashin kulawa ta iyaye da rashin sa ido akan harkokin su ne

yake jawo hakan, wasu tsabagen kwadayi ne da rashin kamun kai da zubar da

tsantsar da darajarsu ta ‘ya ‘ya matar ne take jawowa.

Gaskiya bazan taba yarda ace wai karatun littafi yana sa ‘yan mata suna

lalacewa ba, saboda duk wata mace da ta san darajar kanta to in har ta

karanta littafi ina ganin zata yi kokarin kare mutuncin kan ta ta yi kokarin kai

budurcinta gidan mijinta, saboda ta karanta littafi taga yanda daren farko ya

kasance ga yarinyar littafin, mijinta ya same ta a cikakkiyar mace ta ga irin

tarairaya da

Kulawar da yake bata taga yanda yake sa

mata albarka har da wata dunkuleliyar kyauta da ya yi mata, to ni a ganina

kowace budurwa zata yi sha’awar hakan har ta yi kokarin kai budurcinta gidan

mijinta

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

Abu na biyu ‘yan matanmu za su iya koyon kissa da shagwaba da kalolin girke

girke da yanda ake tarairayar namiji, zasu san abubuwan da suke kara wa mace

ni’ima wanda za su fara tsuma kansu tun kafin su shiga gidan auren, domin

idan ba’a littafin ba babu in da za su sami hakan saboda al’adar Bahaushe da

kunya babu uwar da zata iya zaunar da ‘yarta ta koya mata wa’yannan

abubuwan don zata yi mata aure, za dai ayi wa ‘ya fada ki bi mijinki ki yi masa

biyayya, to kin je kina ta biyayya yana wulakantaki ke baki san dalili ba to duk

wa’yannan abubuwa ne da bakya yi, amma aure ya samu tattali kissa biyan

bukata, shagwaba, ladabi da biyayya, iya girki, iya kwanciya, amfani da turaruka

masu kamshi da na tsugunno, ta cikin ikon Allah za’a samu zaman lafiya da

fahimtar juna a cikin aure.

Shi turaren tsugunno ana amfani da shi ne wajen turare gabanka ka tsugunna

akai hayakin yana shiga ciki to yana kara hade mace ne ya matse ta kamar

amarya.

Jawahir ta kawo gauron numfashi ta ce, “Anty na fahimce ki Allah ka ganar da

yawancin al’umma ko a sami zaman lafiya a tsakanin ma’auratnmu”

“To amin Jawahir.”

Ba jumawa Haidar da Ankul suka dawo suka ci abinci. Ankul ya ce da Anty

maryam ta tashi su tafi gida akwati guda jawahir ta yo wa Anty na tsaraba ta

dakko ta kawo mata suka rinka godiya tare da sa albarka.

Sai da Haidar da jawahir suka yi sati biyu a gidansu suna hutawa basu da aikin

yi sai wasanni da junansu su ci cima me kyau su sha me kyau suke ta sutura

me tsada su bada kamshi su manne da junansu suna faranta ran juna.

Yau sun cika sati biyu da dawowa don haka yau Haidar ya fara fita xuwa office,

jawahir duk ta damu kamar wanda zai je ya yi kwanaki a can sai da ya

lallabeta har da yi mata wayo sannan ya fice. Da yake ya dade rabonsa da

office din dole ya samu ayyuka kaca kaca sun yi masa yawa shi yasa bai samu

sukuni ba, sai na fadawa aiki kawai.

Haidar yana tafiya kuwa jawahir ta dauki mota ta tafi wani hadadden gidan

gyaran jiki tsadadde na ‘ya’yan wane da ‘ya’yan wance, aka yi mata gyaran

gashi aka gyara mata farce aka wanke kafar aka rangada mata kunshin fulawa.

Jikinta ya sha dulka da halawa, jikinta da fuskarta sai wani santsi da taushi

yake yi kamar auduga yana fitar da wani sihirtacce na kyau.

Tana komawa gida kicin ta shiga ta feraye doya ta dora a wuta ta debo

manyan busashen tarwada ta farke cikinta ta kan kare ta kwara masa ruwan

zafi.

Ta hade markade iya ta yi mata abu landa doyar ta dahu ta tsame ta mika wa

iya ta daka mata sakwara, ta hade miyar busashen kifin nan da ta ji onga, kori,

reko, mai da sauren kayan da su ke sa girki armashi, sannan ta cuko zallar

tsokar nama a firinji ta tafasa shi da albasa gishiri da dan magi.

Bayan ya tafasa ta kwankwatsa attaruhu albasa ta dakko tafasashen naman

nan ta hada a turmi ta daka.

Ta ciro shi ta rinka dunkulawa ta fasa kwai ta zuba gishiri onga reko ta dora

manta a wuta ya dau zafi ta rinka daukan dunkulan naman nan tana tsoma sha

a rwan kwan tana sa wa a manta na soyawa, ta gama wannan ta zo ta yanka

salak ta yi masa wanki sosai ta zuba a filet, ta yanyanka tumatur da albasa ta

gewayesu a saman salak da albasar ta kawo dafaffiyar hantarta da ta yi mata

kananan yanka ta zuba a kai.

Bayan ta yada salak, cream ta zuba heinze beans a tsakiya duk wanda ya kalli

hadin salak din dole yawunka ya tsinke, ta debo kayatattun fulas dinta ta zuba

komai taje ta jere su a santara tebir.

Ta debo fararen gobarta manya ta markada ta tace dusar ta markada kankana

da gwanda da ayaba a duk ta tace dusar ta hada akan ruwan gwaibar, ta

daddara rake ta matse ruwan ta hada akai, ta zuba ruwan kwakwa da ruwan

markadaddiyar aya ta zuba madarar ruwa gwangwani biyu ta kawo zumarta me

kyau ta zuba a ciki ta juya ta saka a firinji.38

 

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

By Ismail

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

[Advertisements⬇️]