SALON SO CHAPTER 14
Abin da Haidar yake dauka yawan gajiyar da ita da
yake yi ne shi yake yawan sa mata kasala.
Yau ma tare suka shiga toilet wanka suka yi suka
cuda junansu cikin farin ciki tare da wasanninsu na
ma’aurata. Ya kinkimota ya fito da ita ta zille daga
cikin sa ta koma daya dakin don ta shirya. Haidar ya gama shirin cikin wando iya gwiwa wato tree
gwata da riga marar hannu me kyau yana ta kyalli
don shima fatarsa ta kara gogewa. Kowa ya kalli
shi yasan fatarsa ta kara goge da hutu da jin dadi
irin na masu da shi.
Jawahir ta gama shirinta wani mini siket iya cinya da ya matse mata cinyoyi sai dai yana da tsaga
gaba da baya.
Rigarta iya kirjinta ta tsaya cibiyarta a waje ta ke
fuskarta ta kara haske da kyau da kuruciya
yarintarta ta kara fitowa fili. Jikinta sai fitinannen
kamshi ne yake tashi me ta da sha awa. Ta dawo dakin da ta bar shi saboda zazzabi da ta
ke ji ga ta shin zuciya, yana tsaye yana fesa turare
ta zo ta kwanta a bayansa tare da zagaye shi da
hannuwanta ya kamo ta ya zagayo da ita gabansa
tare da cewa “Bebina lafiya me yake faruwa ne da
ke, jikinki duk ya canja ga yawan lalaci da bacci.? Ya dauke ta suka koma kan kujera suka zauna
yana lallatse jikinta don ganin ta kamaimai me yake
damunta, duk ta narke a jikinsa ta langabe tana ta
zuba masa shagwaba tare da marairaita.
“Bebina muje asibiti a duba min ke don na san me
yake damunki. Cikin ma rairaita ta ce “My love ni bana so muje
asibiti don kada suyi min allura idan na sha fanadol
ma zan samu sauki” Ya ce “Haba bebyna ya za ayi
na barki haka kin ji jikinki kuwa yanda ya dau zafi
ya kama lallatsa wayar likitan Hotel din ta rike
hunnansa kamar za tayi kuka. Don Allah “My love kada ka kirawo shi wallahi na
sha magani zan ji garau. Ya ce ke dai kin fiye tsoron
Allura.”
Ya hada mata break yana bata a hankali tana kau
da kai alamar ba ta so don bata jin dadinsa ya rinka
lallaba ta yana ririta ta har ya samu ta dan ci. Ya bata magani ta sha ta kwanta a jikinsa tana dan yi mata
tausa tare da mammatsa mata jikinta.
Bacci ya kuma dauke ta ya gyara mata kwanciya a
jikinsa lokacin da ta tashi jikin nata da sauki daga
nan London suka wuce kasar America jawahir tayi
mamakin yanda taga Amerika ashe itama haka take da kyau gaskiya kasar ta bata sha awa.
Nan ma Haidar ya bude bakin aljihu yai ta narka
mata kudi kamar vai san zafin nema ba. Watan su
daya a Amerika suka dire kasar Saudiya jawahir
tayi kyau har taga ji da kyau ta kara haske da
kuruciya, duk wanda ya kalle ta zai gano yaron ciki a jikinta don wani dan ya cewa da ta yi da wani
shirtaccen kyau da ta kara, nonuwanta sun sake
cikowa suna tsaye kyam da su. Haidar yana ji da ita
yana lailanta duk da canjawar da jawahir ta yi
hakan bai sa Haidar ya gano ajiyar da ya yi a jikinta
ba, bare ita da kuruciya ta yi mata yawa ita dai tana jin canji a jikinta amma bata dauke shi a komai ba,
bare ta kula.
Suna ta shirye shiryen dawowa gida sun sayi
tsaraba ta ‘yan uwa da abokan arziki kamar masu
shirin bude kamfanin sutura, da kayan kyale kyale.
Jawahir tana kwance lamo a kan gado zazzabi ne me zafi ya rufe ta lokaci daya Haidar ya shigo ya
zauna gefen gadon yana cewa kasa uwar bacci ba
dai daga wannan ‘yar fitar tawa har kin koma
baccinba.?
Ya sa hannu zai dago ta ya ji jikinta da zafi. A gigice
ya dako ta ya rungume ta a jikinsa yana jero mata tambayoyi “Bebina me ya same ki daman vaki da
lafiya, baki gaya min ba daurewa kawai kika yi?”
Bai jira amsar ta ba ya sabe ta a kafada ya yi waje
da ita, motar Hotel din ya yi amfani da ita ta xuwa
asibitin.
Likita Bilkisu muhd Adam ta karbe ta cikin gaggawa ta shiga yi mata tambayoyi da gwaje
gwaje a lokacin ta yi mata sukanin ta hango
karamin ciki dan wata uku a jikinta.
Haidar ya
juyo cikin farin ciki ya dako kan jawahir yasa
harshensa yana lashe hawayen nata. Yasa hannunsa kasar mararta yana dan shafawa ya
rada mata a kunnenta babyna mu duka mun yi
kuruciya da wauta sai dai mu kiyaye gaba sai dai mi
ta addu’a Allah ya raya mana Bebinmu Allah ya fito
mana da shi lafiya.”
Ta ce, “Amin cikin shagwaba ta ce ka huce my love.”
Ya sake rungumarta na hakura bebina tun da ke
ma ba laifinki ba ne na mune da rashin kulawarnu.
Nan fa sabon tattali da ririta suka tashi don Haidar
daga kansa yake yiwa jawahir wanka wai don
kada ta wahala duk wani abu da take yi masa yanzu shi ya dauke mata nauyinsa. Ita kuma ta kan
shagwabe masa ta ce yana ta aikin lada haka yake
so ta zauna ba nono.
Ya ce “Ai aikin lada da yawa yi min kiss shima lada
zaki samu. Ya turo mata kumatu ta cije shi ya da fe
wajen a’a a’a bazan yarda ba sai na rama. Da ya yi kanta zai turmusheta sai ta daga hannu
sama tana cewa bebinka bebinka zaka wahalar
dashi ya yi dariya ya dumgure ta.”
Ta yi dariya don Allah yaya mu goma gida mana.
Ya zaro ido “Ke yaushe zan yarda mu shiga jirgi da
wannan dan ta yin cikin nawa.” Salon kisa wabi abun ya faru da shi ai mu da mu
koma gida sai kin haihu su ganmu da bebinmu. Ta
marairaice ta fada jikinsa ta saka kuka ya dagota
yana dariya to to sarkin shagwaba yi shiru da
gangan nake yi rana ita yau jirgin mu zai daga
zuwa Nigeria Ta kuma kankame shi tana kyal kyala dariya,
Haidar ya gama luguiguita jawahir dukjansu zube a
gado suna mayar da numfashi.
Hannun Haidar yana kasan marar jawahir yana
shafa bebinsa.
Ya ce ko kin san wani abu? Ta girgiza kai ya ce sai da likitan nan ta fara gaya min kina da cikinsa nan
na gani alamomin hakan daga jikinki. Ga shi yanzu
har ya fara fitowa kamar ba dan wata hudu ba, ta
marairaice murya cikin shagwaba ta ce wallahi ni
kunya nake ji su ganni da cikib nan ai sai suce vani
da kunya daga zuwa jinya, na koma da dan rakiya. Haidar ya dada jawo ta jikinsa yana shafa bayinta
tare da dariya yace in banda abinki ni shi ne shedar
na warke.
“Kinga duk wanda ya kalle ki ba sai ya tambaye mu
an samu nasarar aiki ko ba’a samu ba, ta dada
shigewa jikinsa ta ce yanzu shi kenan kowa yasan abin da muka yi ko?
Ya kara tun tsirewa da dariya yanzu bebina in
banda abin ki akwai wanda ya taba sha a ruwa
ne?” Kowa kika ganshi da ciki ai ta haka ya samu ta
ce “Na shiga uku yanzu momyna da Dadyna da
Anty da Inna da Abbanka haka za su ganni da ciki gaskiya zan sha kunya kai ku wa ka yi min wayyo
babu ruwanka ko?
Washegari jirginsu ya daga zuwa Nigeria da yake
an san da dawowarsu ‘yan uwa iyayensu sun zo
taryarsu babu wanda yasan jawahir tana da ciki sai
dai idonsu ya gane musu. A cikin jirgi, jirgi yana jama’a aka fara sakkowa,
Haidar ne a gaba jawahir tana biye da shi sun yi
kyau sun dade kara ja da fari jin dadi da hutu ya sa
sun haske wajen kowa ya kalle su sai ya sake
duban su ba don murmushin da su ke dokawa ba,
da iyayensu basu gane su ba. Suna sakkowa jawahir zata kwasa da gudu ganin iyayenta Haidar
ya riko ta yana ce matw ki kula kada ki yi min
ganganci da ciki.”
‘Yan uwa suka yunkuro gaba daya suka taro su
jawahir ta durkusa kasa ta kama kafar babanta ta
rike tana me jin dadi da murnar ganinsu. Ya sa hannu ya dagota yana kallonta fuskarsa cike
da murmushi na yanda yaga ‘yarsa ta kwantar da
hankalinta gashi yanda ta kara kyau da haske
kamar balarabiya.
Inna ta dafa kafadarta jawahir ta juyo ta rungume
ta tana murna Inna ta dako ta cikin dariya ta ce ke taurin me nake ji haka? Ko dai kin samo mana dan
London? Kai amma abu ya yi kyau.”
Dady ya ce “Menene?”
Inna ta ce, “Ciki ne da ita da sauri jawahir ta fuzge
jikinta cikin jin kunya taje ta rungume Mominta da
Antinta, ta je ta gaisa da Abban Haidar. Nan fa sukai ta gaisawa da ‘yan uwa ana murnar
ganin juna. Daga nan suka rankaya gaba daya don
raka su gidansu. Jawahir ta yi mamakin canja
fasalin gidan nasu da aka yi, ya yi masifar tsaruwa,
don ya fi na da ma kyau, tsadaddun kujerun da
kayan kyale kyalen da suka suyo a kasar waje. An kawata babban falon da su, sai ka ce falon
sarauniya America don tsananin tsaruwa da kyau
da ya yi sai da aka ci aka sha sannan iyayensu suka
taya su murnar samun lafiyar. Haidar da karuwar
da suka samu.
Kowa ya fashe, sun tattafi ma’aikatan gidan suka kara gyara gidan ko ina ya kara yin fes sai sheki da
kyalli ne yake tashi da hadadden kamshi.
Da daddare “Faruk ya zo suka rungume juna shi da
Haidar suna murnar sake ganin juna.36