SALON SO CHAPTER 14

SALON SO CHAPTER 14

 

 

Abin da Haidar yake dauka yawan gajiyar da ita da

yake yi ne shi yake yawan sa mata kasala.

Yau ma tare suka shiga toilet wanka suka yi suka

cuda junansu cikin farin ciki tare da wasanninsu na

ma’aurata. Ya kinkimota ya fito da ita ta zille daga

cikin sa ta koma daya dakin don ta shirya. Haidar ya gama shirin cikin wando iya gwiwa wato tree

gwata da riga marar hannu me kyau yana ta kyalli

don shima fatarsa ta kara gogewa. Kowa ya kalli

shi yasan fatarsa ta kara goge da hutu da jin dadi

irin na masu da shi.

Jawahir ta gama shirinta wani mini siket iya cinya da ya matse mata cinyoyi sai dai yana da tsaga

gaba da baya.

Rigarta iya kirjinta ta tsaya cibiyarta a waje ta ke

fuskarta ta kara haske da kyau da kuruciya

yarintarta ta kara fitowa fili. Jikinta sai fitinannen

kamshi ne yake tashi me ta da sha awa. Ta dawo dakin da ta bar shi saboda zazzabi da ta

ke ji ga ta shin zuciya, yana tsaye yana fesa turare

ta zo ta kwanta a bayansa tare da zagaye shi da

hannuwanta ya kamo ta ya zagayo da ita gabansa

tare da cewa “Bebina lafiya me yake faruwa ne da

ke, jikinki duk ya canja ga yawan lalaci da bacci.? Ya dauke ta suka koma kan kujera suka zauna

yana lallatse jikinta don ganin ta kamaimai me yake

damunta, duk ta narke a jikinsa ta langabe tana ta

zuba masa shagwaba tare da marairaita.

“Bebina muje asibiti a duba min ke don na san me

yake damunki. Cikin ma rairaita ta ce “My love ni bana so muje

asibiti don kada suyi min allura idan na sha fanadol

ma zan samu sauki” Ya ce “Haba bebyna ya za ayi

na barki haka kin ji jikinki kuwa yanda ya dau zafi

ya kama lallatsa wayar likitan Hotel din ta rike

hunnansa kamar za tayi kuka. Don Allah “My love kada ka kirawo shi wallahi na

sha magani zan ji garau. Ya ce ke dai kin fiye tsoron

Allura.”

Ya hada mata break yana bata a hankali tana kau

da kai alamar ba ta so don bata jin dadinsa ya rinka

lallaba ta yana ririta ta har ya samu ta dan ci. Ya bata magani ta sha ta kwanta a jikinsa tana dan yi mata

tausa tare da mammatsa mata jikinta.

Bacci ya kuma dauke ta ya gyara mata kwanciya a

jikinsa lokacin da ta tashi jikin nata da sauki daga

nan London suka wuce kasar America jawahir tayi

mamakin yanda taga Amerika ashe itama haka take da kyau gaskiya kasar ta bata sha awa.

Nan ma Haidar ya bude bakin aljihu yai ta narka

mata kudi kamar vai san zafin nema ba. Watan su

daya a Amerika suka dire kasar Saudiya jawahir

tayi kyau har taga ji da kyau ta kara haske da

kuruciya, duk wanda ya kalle ta zai gano yaron ciki a jikinta don wani dan ya cewa da ta yi da wani

shirtaccen kyau da ta kara, nonuwanta sun sake

cikowa suna tsaye kyam da su. Haidar yana ji da ita

yana lailanta duk da canjawar da jawahir ta yi

hakan bai sa Haidar ya gano ajiyar da ya yi a jikinta

ba, bare ita da kuruciya ta yi mata yawa ita dai tana jin canji a jikinta amma bata dauke shi a komai ba,

bare ta kula.

Suna ta shirye shiryen dawowa gida sun sayi

tsaraba ta ‘yan uwa da abokan arziki kamar masu

shirin bude kamfanin sutura, da kayan kyale kyale.

Jawahir tana kwance lamo a kan gado zazzabi ne me zafi ya rufe ta lokaci daya Haidar ya shigo ya

zauna gefen gadon yana cewa kasa uwar bacci ba

dai daga wannan ‘yar fitar tawa har kin koma

baccinba.?

Ya sa hannu zai dago ta ya ji jikinta da zafi. A gigice

ya dako ta ya rungume ta a jikinsa yana jero mata tambayoyi “Bebina me ya same ki daman vaki da

lafiya, baki gaya min ba daurewa kawai kika yi?”

Bai jira amsar ta ba ya sabe ta a kafada ya yi waje

da ita, motar Hotel din ya yi amfani da ita ta xuwa

asibitin.

Likita Bilkisu muhd Adam ta karbe ta cikin gaggawa ta shiga yi mata tambayoyi da gwaje

gwaje a lokacin ta yi mata sukanin ta hango

karamin ciki dan wata uku a jikinta.

Haidar ya

juyo cikin farin ciki ya dako kan jawahir yasa

harshensa yana lashe hawayen nata. Yasa hannunsa kasar mararta yana dan shafawa ya

rada mata a kunnenta babyna mu duka mun yi

kuruciya da wauta sai dai mu kiyaye gaba sai dai mi

ta addu’a Allah ya raya mana Bebinmu Allah ya fito

mana da shi lafiya.”

Ta ce, “Amin cikin shagwaba ta ce ka huce my love.”

Ya sake rungumarta na hakura bebina tun da ke

ma ba laifinki ba ne na mune da rashin kulawarnu.

Nan fa sabon tattali da ririta suka tashi don Haidar

daga kansa yake yiwa jawahir wanka wai don

kada ta wahala duk wani abu da take yi masa yanzu shi ya dauke mata nauyinsa. Ita kuma ta kan

shagwabe masa ta ce yana ta aikin lada haka yake

so ta zauna ba nono.

Ya ce “Ai aikin lada da yawa yi min kiss shima lada

zaki samu. Ya turo mata kumatu ta cije shi ya da fe

wajen a’a a’a bazan yarda ba sai na rama. Da ya yi kanta zai turmusheta sai ta daga hannu

sama tana cewa bebinka bebinka zaka wahalar

dashi ya yi dariya ya dumgure ta.”

Ta yi dariya don Allah yaya mu goma gida mana.

Ya zaro ido “Ke yaushe zan yarda mu shiga jirgi da

wannan dan ta yin cikin nawa.” Salon kisa wabi abun ya faru da shi ai mu da mu

koma gida sai kin haihu su ganmu da bebinmu. Ta

marairaice ta fada jikinsa ta saka kuka ya dagota

yana dariya to to sarkin shagwaba yi shiru da

gangan nake yi rana ita yau jirgin mu zai daga

zuwa Nigeria Ta kuma kankame shi tana kyal kyala dariya,

Haidar ya gama luguiguita jawahir dukjansu zube a

gado suna mayar da numfashi.

Hannun Haidar yana kasan marar jawahir yana

shafa bebinsa.

Ya ce ko kin san wani abu? Ta girgiza kai ya ce sai da likitan nan ta fara gaya min kina da cikinsa nan

na gani alamomin hakan daga jikinki. Ga shi yanzu

har ya fara fitowa kamar ba dan wata hudu ba, ta

marairaice murya cikin shagwaba ta ce wallahi ni

kunya nake ji su ganni da cikib nan ai sai suce vani

da kunya daga zuwa jinya, na koma da dan rakiya. Haidar ya dada jawo ta jikinsa yana shafa bayinta

tare da dariya yace in banda abinki ni shi ne shedar

na warke.

“Kinga duk wanda ya kalle ki ba sai ya tambaye mu

an samu nasarar aiki ko ba’a samu ba, ta dada

shigewa jikinsa ta ce yanzu shi kenan kowa yasan abin da muka yi ko?

Ya kara tun tsirewa da dariya yanzu bebina in

banda abin ki akwai wanda ya taba sha a ruwa

ne?” Kowa kika ganshi da ciki ai ta haka ya samu ta

ce “Na shiga uku yanzu momyna da Dadyna da

Anty da Inna da Abbanka haka za su ganni da ciki gaskiya zan sha kunya kai ku wa ka yi min wayyo

babu ruwanka ko?

Washegari jirginsu ya daga zuwa Nigeria da yake

an san da dawowarsu ‘yan uwa iyayensu sun zo

taryarsu babu wanda yasan jawahir tana da ciki sai

dai idonsu ya gane musu. A cikin jirgi, jirgi yana jama’a aka fara sakkowa,

Haidar ne a gaba jawahir tana biye da shi sun yi

kyau sun dade kara ja da fari jin dadi da hutu ya sa

sun haske wajen kowa ya kalle su sai ya sake

duban su ba don murmushin da su ke dokawa ba,

da iyayensu basu gane su ba. Suna sakkowa jawahir zata kwasa da gudu ganin iyayenta Haidar

ya riko ta yana ce matw ki kula kada ki yi min

ganganci da ciki.”

‘Yan uwa suka yunkuro gaba daya suka taro su

jawahir ta durkusa kasa ta kama kafar babanta ta

rike tana me jin dadi da murnar ganinsu. Ya sa hannu ya dagota yana kallonta fuskarsa cike

da murmushi na yanda yaga ‘yarsa ta kwantar da

hankalinta gashi yanda ta kara kyau da haske

kamar balarabiya.

Inna ta dafa kafadarta jawahir ta juyo ta rungume

ta tana murna Inna ta dako ta cikin dariya ta ce ke taurin me nake ji haka? Ko dai kin samo mana dan

London? Kai amma abu ya yi kyau.”

Dady ya ce “Menene?”

Inna ta ce, “Ciki ne da ita da sauri jawahir ta fuzge

jikinta cikin jin kunya taje ta rungume Mominta da

Antinta, ta je ta gaisa da Abban Haidar. Nan fa sukai ta gaisawa da ‘yan uwa ana murnar

ganin juna. Daga nan suka rankaya gaba daya don

raka su gidansu. Jawahir ta yi mamakin canja

fasalin gidan nasu da aka yi, ya yi masifar tsaruwa,

don ya fi na da ma kyau, tsadaddun kujerun da

kayan kyale kyalen da suka suyo a kasar waje. An kawata babban falon da su, sai ka ce falon

sarauniya America don tsananin tsaruwa da kyau

da ya yi sai da aka ci aka sha sannan iyayensu suka

taya su murnar samun lafiyar. Haidar da karuwar

da suka samu.

Kowa ya fashe, sun tattafi ma’aikatan gidan suka kara gyara gidan ko ina ya kara yin fes sai sheki da

kyalli ne yake tashi da hadadden kamshi.

Da daddare “Faruk ya zo suka rungume juna shi da

Haidar suna murnar sake ganin juna.36

About Ismail

Check Also

BAKAR INUWA CHAPTER 23

Ganin taÆ™i cin komai Anne ta kira sunanta. Ta É—ago domin amsawa taci karo da …

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *