[Advertisements⬇️]

SALON SO CHAPTER 12 - Bankinhausanovels
Mon. Mar 27th, 2023

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

SALON SO CHAPTER 12

 

 

 

 

Jikinta ya rinka rawa da karkarwa kamar mazari. Ta

kasa wani katabus sai kuka data ke yi tana yi masa

magiyar daya hakura ya kyale ta.

Haidar kuwa kusan ma iya cewa hankalinsa baya

jikinsa saboda samvatu da ya rinka yi yana surutai.

Hankalin jawahir ya tashi, ta rinka dukan Haidar tana girgiza shi yayin da ta tsala wata kara shi

kenan Haidar ya cika aiki.

Sai da Haidar ya gama samun nutsuwa hankalinsa

ya dawo jikinsa sannan ya kula da halin da jawahir

take ciki sai nishi take yi sama-sama fuskarta da

fulon da ta ke kai sun jike da gumi da hawaye. Inna lillahi wa’inna ilaihir raji’un, ya dago ta yaga ta

koma ta langabe a hankali ya ajiye ta a gadon ya

nufi tolet ya cika baho da ruwan zafi ya zuba datol

yaje ya dauko ta ya sakata a ruwan zafin ya rinka

buda mata kafafuwanta ruwan zafin yana ratsa ta.

Ita kuwa Jawahir sai ‘yar kara take yi irin ta galabaitar nan da wahala. Haidar kamar zai yi kuka

saboda tsananin tausayinta. Sau uku yana canza

mata ruwan ya karanta mata niyyar wanka ta fada

a zuciyarta, ya yi mata wankan tsarki shima ya yi

yana dota a tawul ya kawo ta dakin ya zira mata

doguwar riga shima yasa jallabiya. Ya dauki waya ya bugawa likitan hotal din cikin

lokacin kankani ya zo ya duba jawahir ya yi mata

allura ya ba wa Haidar magungunan da zai bata

tasha.

Likita ya yi musu sallama ya fita Haidar ya tsiyaye

mata madarar kwali a kofi tana manne a kirjinsa duk ta wani langabe don bata da kuzarin komai sai

tsananin kasala da ciwon jiki ga radadi da yake

damunta.

Ya dago kanta ya sa mata kofin a bakinta ta

langabe cikin shagwaba ta ce ni bazan iya sha ba,

yi hakuri bebi na dan sha kurbi kadan kin ji kinga magani zaki sha don jikinki ya wartsake

Ta kurba ta hadiye da kyar, ta kau da kai, “Yi hakuri

dan kara kadan kinji bebi na.

Da lallashi da lallama ta dan sha da yawa ya bata

maganin da ruwa ta sha ya dauke ta suka koma

daki lokacin karfe biyu na dare, ya kwanta a gadon ya dorata a kirjinsa ya rungume ta tana ta faman

raki wayyo yayana bayana kuguna kaina yaya

ko’ina ciwo yake yi min

“Sannu bebi na Allah ya yi miki albarka hakika kin

cika ‘yar halak da ki ka kawo min budurcinki lafiya.

Allah ya yi miki albarka Allah ya saka miki da alheri. Ubangiji ya bamu zuri’a ta gari.”

Ya rinka shafa bayanta yana yi mata tausa kadan-

kadan, yana mammatsa mata jikinta bacci ya

dauketa. Haidar ya rungume ta ya kankame kamar

wani zai kwace masa ita, amma maganar bacci

babu ita don tsananin dadi da zumudi ya hana shi gyangyadawa.

Mamaki ne ya cika zuciyar Haidar yanda ya ji

dandanon zumar jawahir yanzu jawahir din da ya

raina ce Allah ya wadata ta da ni’ima haka? Lallai

dan hakin da ka raina shi yake tsone maka idonka.

Yau dai kam ga shi jawahir ta tsone masa idon, lallai Allah yana sonsa da ya dawo masa da jawahir

bayan subuce masa da tayi a baya, Allah ya taimake

shi bai yi wautar sakin ta ba.

Ai dole ne ya tashi ya yi nafila don nuna godiyarsa

ga ubangiji a bisa wannan baiwa da Ubangijin ya yi

masa, na mallaka masa gwarzuwar mata mai cikar halitta da wadatacciyar ni’ima.

A hankali ya zare jawahir daga jikinsa ya kara mata

fulo don kar ta farka ya nufi toilet ya dauro

kyakkyawar alwala ya zo ya fara nafula raka’a

goma sha biyu ya yi wa Annabi salati kafa dubu, ya

daga hannuwansa sama yai ta kwaraea addu’a, yana yiwa Allah kirari da yaba su zaman lafiya da

zuri’a me albarka shi da matarsa jawahir.

Sai da aka yi kiran assalatu ya tashi jawahir suka yi

sallar asuba, suka koma suka kwanta.

Sha daya

na safe Haidar ya farka ya zare jikinsa a hankali ya nufi toilet ya fara wanka

Jawahir ta bude idonta ta tashi ta daddogara a

hankali ta fito daga wannan dakin ta shiga dayan

itama ta fada toilet

Da yake falo ne da dakuna biyu a cikin falon wanda

suka kama. Jawahir ta fito daga wanka ta tsane jikinta da tawul,

ta shafe jikinta da hadaddun mayukanta masu

kamshi da sa taushin fata hade da santsin jiki. Ta

rinka mulke gabobinta da hadaddun turaruka na

jiki masu dadin kamshi.

Ta tsala kwalliyar fuskarta yanda yaka mata fuskar sai sheki take yi ta yi sumul sumul abun sha awa.

Ta saka wani tsadaddan farin yadi sol mai dishi-

dishin gwal din a jiki ‘yar karamar riga ce fitet me

dan guntun hannu rigar ta yi mata cif a jikinta. Sai

siket din da ya yi mata tsantsan duk wata sura ta

jikinta ta bayyana ba ma kamar kirjinta da yake cike da dukiyar fulani a tsattsaye suna barazanar

tsokane idon me kallon su. Ta sha adon gwal yari

da sarka manya ga awarwaro da zobuna tuni ta

dauki kyalli tana sheki

Tasa farin takalmi tana fesa turare ta ji dhigowar

Haidar ta yi saurin boyewa a cikin labulaye: Haidar shima ya shirya cikin wani lafiyayyen boyel fari kal

me laushi sai fitinan nan kamshi ne yake tashi a

jikinsa kamar ya yi barin turare.

Ya shigo dakin ya kama wara ido don ganin in da

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

zai hango tauraruwarsa ga shi dai duk kamshinta

ya cika dakin. Kafarta ya hango ta kasan labulan ya nufo wajen

ya janye labulan tasa hannu rufe fuskarta. Ya tsane

yana karo mata kallo cikin zafaffiyar kaunarta da

matsananciyar sha’awarta.

Ya jawo ta jikinsa ya manne ta a kirjinsa yayin da

kaunar ta take dada ratsa zuciyarsa. Cak ya dauke ta yayo falo da ita suka zube akan

kafet don karyawa, tana makale a jikinsa shi ji yake

ina ma zai iya tsaga jikinsa ya tura ta ciki da sai ya fi

masa sauki da yanda kaunarta take addabarsa a

zuciyarsa.

A baki ya rinka ba ta break din cikin lallashi da lallama don shi da da hali ma tauna mata zai rinka yi

don ta samu saukin hadiya.

Sai da ya tabbatar ta koshi sannan ya rabu da ita

shima ya ci ya yi kat.

Ya shiga wasanni da sassan jikinta in da ita kuma ta

takure waje daya ta ki bude fuskarta. Ya dauke ta cak ya yi gado da ita yana cewa “To

bari mu maimaita abun jiya tun da kin fi so ko?’

Cikin marairaitar murya ta ce, “Wayyo Yaya don

Allah ka kyale ni bana so yayin da ta kwabe fuska

take kokarin yin kuka.

Ya rungume ta “Sorry bebi na kada ki yi kuka da gangan nake yi miki. Rufe idonki, “Ta rufe yayin da

ya saka mata ‘yar batta guda biyu manya a hannun

nata duk ya bude su.

Ya ce ta bude idonta tana budewa taga custume

yari da sarka da zobe manya tafka tafka kirar dubai

sarkar mai harafin H/J, sai daya battar kuma manyan warwaraye ne guda hudu gaba daya

Daimond kudinsu a kalla zasu yi dubu dari biyar da

doriya.

Bude baki tare da kwalalo ido ta ce “Yaya wannan

fa?

“Kyauta ce nayi miki don farin cikin yanda na riske ki.

Ta kankame shi cikin murna yayin da ta lalubi

bakinsa ta yi masa kyakkyawar sumbata, ta ce

“Yaya na gode Allah ya saka maka alheri Ubangiji

ya raba ka da sharrin makiya.” Ya ce “Amin babyna,

na gode da addu’arki Allah yasa mun samu rabon bebi a daren jiya ko kuma in an jima mu samu.”

Cikin shagwaba ta bigi kirjinsa “Um, um ni dai yaya

ba za’a kuma ba da ciwo.”

“To shi kenan kada ki yi min kuka ma arahar

hawaye.”

“Yaya ya aka yi ka samu masu harafin sunanmu.?” Ya ce, “Ai tun ranar da muka fara ziyartar asibitin

kafin ayi min aikin nan naje gurin da suke kerawar

nasa su kera min don zuwan wannan rana.

“Kai Yaya amma kuwa na gode Allah ya saka da

alheri

Ya dora hannunsa akan bakinta ya ce “Shit bana son yawan godiyar nan kuma ki cire wannan

Yayan da kike gaya min bana so.

Cikin kashe murya da kissa ta ce, “To me zan dinga

ce maka?

“Ke za ki zabo da kanki ki rada min.

Ya kawo kunnansa daidai bakinta “To gaya min naji”.

Cikin kasa kasa da murya ta ce, “My love yayi

maka?”

Ya rungume ta yana ihun murna yayi ya yi kwarai

babyna kin iya zaben suna. Ta rufe idonta tana

dariya. Ta kama lumshe ido irin na me jin bacci. Ya ce, “Bacci babyna.?” Ta daga kai kwantar da ita a

kan gadon to kwanta na yi miki tausa.

A hankali ya rinka yi mata tausar yana dan matsa

mata jikinta. Sannu a hankali bacci yayi awon gaba

da ita ya zuba mata ido yana kallon tsabagen kyau

da Allah ya bata. Ga komai nata cif-cif ba abin da ya fi ba shi mamaki yanda ya jita tamtsan cike da

ni’ima ga kirjinta cike da dukiyar fulani abun da yafi

sha’awa da daukar hankalinsa a jikinta.

Shima kwanciyar ya yi ya manne a jikinta ya

kankame ta har sai da ta yi ‘yar kara ta ce my love

sannan ya sassauta mata rikon. Sai bayan Azahar suka tashi suka sake sabon wanka tare da yin

alwala ya ja musu limanci suka yi sallar Azahar.

Daga nan suka sake sabon shiri shigar kananan

kaya suka yi ke in kin gansu sai ki zata Indiyawa

ne. Suka ci kayataccen abinci me rai da lafiya,

Haidar ya jawo ta jikinsa babyna mu dan fita mu zaga gari ko? In nuna miki wajajen ban sha awa da

na kayatarwa.

Ta noke a jikinsa tare da cewa “my love ka bari sai

gobe jikina har yanxu yana yi min ciwo.”

“Ciwo babyna! Kada fa ya kawo mana matsala in an

jima fa.? Ta bigi kirjinsa cikin wasa tana harararsa, “Allah

Allah my love ka bari zan yi maka kuka.

To na bari na bari babyna, tana langabe a jikinsa sai

shagwaba take yi masa du ta wani narke masa sai

zuba masa sangarta. Shi kuwa gogan ya rikice duk

ta burkita masa tunani da sha’awarta sai riritata yake yi yana lallaminta, tare da taba wasanni a

jikinsa nata ko zai samu ‘yar nutsuwa kwana hudu

yana jirarta ba tare da ya kuma neman yin wani

abu da ita ba, sai yai ta faman riritata yana

sangartata yayin da take zuba masa shagwaba son

ranta shi kuwa yai ta biye mata don bata da masaukin da ya wuce jikinsa, ko yaushe tana

manne a jikinsa yanayi mata tausa ko wasanninsu

na ma’aurata.

Aha har yanxun xa’a bani ko kuwa sai na kuuma?

Idan kuuma ba’a bani ba………… hmmmmmmmmm

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

By Ismail

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

[Advertisements⬇️]