[Advertisements⬇️]

SALON SO CHAPTER 11 - Bankinhausanovels
Fri. Mar 31st, 2023

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

SALON SO CHAPTER 11

 

 

 

Ya kashe fitilar ya hau gadon ya shiga cikin

bargon ya sa hannu ya shafo ta. Cikin razana ta

farka a firgice ta yi zumbur ta mike tsorace tana

wayyo Allah na Yaya na shiga uku, wayyo Allah

yaya na ka zo ka cece ni.” Ya mike shi ma ya

riko ta, ta dada firgicewa tare da sa kuka, “Wayyo

na shiga uku yaya ka zo ka cece ni.” Ya ce,

“Jawahir meye haka? Ni ne fa Yayanki Haidar ba

ki gane ni ba ne? Ya kunna fitila ta daga kai ta

kalle shi ta mayar dakanta kan kirjinsa ta kwantar

tana ajiyar zuciya. Ya sa hannu ya zagaye ta ya

kashe fitilar ya yi gadon da ita. Ya kwanta tana

manne a jikinsa, jikinta sai bari yake yi na

tsoratar da ta yi.

Zuciyar Haidar fes yau ga shi manne da jawahir

dinsa, abar sonsa shi kuwa ya taba jin jiki me

taushi da santsi kamar na jawahir dinsa? Shi dai

bai gushe ba yana sambatu da jin dadin tattausar

jiki har bacci ya kwashe shi.

Da asuba ya riga ta tashi sai da ya dauko alwala

sannan ya tashe ta ta tafi yo alwala kafin ta

dawo ya tayar da raka’atainil fajri ita ma ta tayar

suna idarwa suka tayar da sallar asuba Haidar ya

ja musu limanci.

Suna idarwa suka ja carbi suka yi ta yin addu’a

har suka shafa ya bude musu kur’ani suka biya

tare suka sake yin addu’a suka shafa.

Ta durkusa gabansa yaya ina kwana. Ya amsa

cikin murmushin jin dadi kin kwana lafiya yaya

tsoro? Ta yi murmushi ta mike ya ce, “Ina za ki?

Sai da ta rissana sannan ta ce, “Kicin za ni. Ya

ce “A’a taho kwanciya za mu yi suka koma gado

suka kwanta.

Bacci ya dade da kwashe su wani gigitaccen bugu

ne ya farkar da su a wahalce Haidar ya zare

jikinsa daga na jawahir ya mike ya nufi kofar ya

bude. Kausar ce ta cukuikuye masa wuyan riga

tana cewa, “Kai wallahi sai ka sake ni takardarta

za ka ba ni ba zan iya zama da miskini ba.

Ya wankawa fuskarta mari ya ce, “Ni kika

shakarwa wuyan riga, dan iska za ki mayar da

ni? An ki a sake ki din ki je ki gayawa duk wanda

za ki gayawa. Ta dafe kunci ni ka mara to

wallahi sai ka gane kurenka. Ta juya ta yi dakinta

ta dauko mayafi ta yi waje ta hau mota ta tuka

kanta ta fice daga gidan.

Kotu ta nufa ta shigar da kara.

Haidar yana gida sun gama shirinsu sun ci

kwalliya kamar masu xuwa fati, sun gama

karyawa ke nan yaron gidansa ya yi sallama a

kofar falon aka amsa masa ba tare da ya shiga

ba ya ce Yallabai ana sallama da kai a waje.

Ya ce, “Okey ga ni nan fitowa.

Ya mike ya fita

Da mamakinsa suka gaisa da bako ba tare da ya

san shi ba. Bako ya mika masa zungureriyar

takarda, “Ni yaron alkali ne ga shi wannan

sammaci ne daga kotu matarka tana kararka.

Haidar ya rinka juya takarda a hannunsa cikin

mamaki ya ce, “Okey je ka na gani. Yaron alkali

ya juya ya tafi, Haidar ya shiga gida

Ya cewa jawahir zai je gida yanzu Abbansa yana

son ganinsa. Ta yi masa kyakkyawar addu’a tare

da fatan Allah ya dawo da shi lafiya.”

A hankali ya rinka juya motar yana mamakin hali

irin na kausar. Yana isa gida ya samu Abbansa a

falo da Anti suka gaisa sai ya mikawa Abbansa

takardar da aka kawo masa ya ware takardar ya

karanta. Abba ya hangame baki tare da yin

salati. Cikin yaya? Me ya hada ku? Haidar ya

kwashe labarin komai ya gaya masa. Abba ya

kama salati amma wannan yarinya ta ci mana

mutunci. Anti ta ce ka sake ta kawai ba sai an je

gaban kotu ta tsinka mu ba.

Nan take Haidar ya rubuta mata takardar saki

daya Anti ta karba ta bawa me aikinta tace ta yi

sauri ta je direba ya kai ta gidan Saddika kawar

Kausar su kaiwa Kausar din.

Kausar kuwa tana ganin takarda ta cika da farin

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

ciki inda a nan take ta yi wa alkalin waya ta ce

ta janye shari’ar ta yi sauri ta koma gidan Haidar

daman ta sa ‘yan matanta sun hada mata

kayanta na sawa da duk wani abu na amfaninta

na kwalliya suka judo mata akwatunanta suka

loda su a but direba ya je su zuwa Airport suka

yanki tikiti suka nufi Abuja.

Abbab Haidar ya dube shi ya ce, “Bana so ka sa

damuwa a ranka bare ka zo abin yana damunka

daman na gama shirya muku tafiya xuwa kasar

waje Kai da

jawahir za ku je asibitin Cairo sabo da haka ku je

ku fara shiri nan da sati daya za ku tafi.

“To Abba mun gode Allah ya saka da alheri

Ubangiji ya kara budi.

Haidar ya koma gida yake gayawa jawahir abin

da ya faru duk da jawahir ba ta son zaman

Kausar a gidan amma ba ta ji dadin sakin da

Haidar ya yi mata ba. Ba su da wani lokaci sai

na shiri da ziyartar ‘yan uwa suna yi musu

sallama.

Ranar da suka je Abuja gidan Ankul Anti Maryam

ta ce ya dai ‘yata in ce ko dai har yanzu kina

shan abubuwan da na gaya miki?

“Ai Anti tun ranar da na bar gidan nan ban yi

fashin shan kayayyakin nan ba, don wasu

abubuwan ma idan na hada har da Yayan muke

sha ba tare da ya san ko meye ba.

“Yauwa diyata na sara miki yanzu na san kin

tsumu kin cika da ni’ima sosai karyar Haidar ya

dandana ki ya kuma kusantar wata matar.

“Allah Auntyna, “Suka tafa. Aunty maryam ta

kwaso mata wasu hadin da ta kuma yi tare da

wani turare na gama da ake yi kafin saduwa da

miji, tsaraba dai sosai ta hada mata don tafiya

Cairo.

Sun je gidan Inna gidan Yagwalgwal, gidan Faruk,

gidansu Bilkisu, gidan Abba, gidan Dady, duk

gidan dangi da ‘yan uwa babu inda ba su ziyarta

ba.

Sha biyu na dare jirginsu ya tashi xuwa kasar

Egypt wato inda za su sauka a birnin Cairo inda

asibitin da za a duba Haidar yake.

Ranar da suka dira gajiya ba ta bar su ba

ramuwar bacci suka yi sai washegari suka isa

asibitin. Aka saka Haidar a computer cikin lokaci

kankani suka gano matsalar ba tare da bata

lokaci ba suka yi masa aiki suka kwantar da shi a

asibitin tsawon sati daya saboda magungunan da

yake sha.

Cikin ikon Allah Haidar ya ware ya samu sauki

kamar ba shi ba. Asibitin sun sallame shi sun

dawo Hotel din da suka sauka. Yana kwance a

kan kafet jawahir tana masa tausa sannu a

hankali yana wash! Wash!! Tare da lumshe ido.

Yau duk ya wani shagwabe mata ya narke mata

ta hana ta sukuni daga ya ce, nan yana cuwo sai

ya ce can. Sai bin sa take da lallama cikin

tausayawa da kyar ta samu ya yi bacci ta shiga

tolet ta yi wanka ta fito ta gyara jikinta da

hadadden mayuka masu kamshi tare da turarukan

da ta mulke jikinta kowacce gaba ta jikinta

kamshi take fitarwa.

Ta saka ‘yar bingilar rigar bacci iya cinya me

hannun shimi ta dada feshe dakin da Air

freeshner. Dakin ya dau sanyi da daddadan

kamshi ta haye gado ta shiga bargo ba ta jima ba

bacci ya yi awon gaba da ita.

Haidar da idonsa yake a kanne yana kallonta ya

mike shi ma ya shiga tolet ya watsa ruwa ya fito

ya gama shirinsa ya hade jikinsa da kamshin

turare, ya kashe fitila ya hau gadon ya kunna dim

night dakin ya yi shiru ba ka jin motsin komai sai

karar A.C Haidar ya manne ta a kirjinsa ya matse

ta gam, ya tura harshensa cikin bakinta ya rinka

tsotsa yana wani salo na daban. Da ya gangaro

zuwa kirjinta yayin da ya zare karamar rigar da

take jikinta.

Bayyanar na shanunta a waje shi ya kara gigitar

da shi jikinsa ya hau bari da rawa ya gigice ya 33

dimauce har ya manta a wacce duniyar yake.

[Advertisements⬇️]

[Continue Reading⬇️]

By Ismail

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

[Advertisements⬇️]