[Advertisements⬇️]
[Continue Reading⬇️]
SALON SO CHAPTER 11
Ya kashe fitilar ya hau gadon ya shiga cikin
bargon ya sa hannu ya shafo ta. Cikin razana ta
farka a firgice ta yi zumbur ta mike tsorace tana
wayyo Allah na Yaya na shiga uku, wayyo Allah
yaya na ka zo ka cece ni.” Ya mike shi ma ya
riko ta, ta dada firgicewa tare da sa kuka, “Wayyo
na shiga uku yaya ka zo ka cece ni.” Ya ce,
“Jawahir meye haka? Ni ne fa Yayanki Haidar ba
ki gane ni ba ne? Ya kunna fitila ta daga kai ta
kalle shi ta mayar dakanta kan kirjinsa ta kwantar
tana ajiyar zuciya. Ya sa hannu ya zagaye ta ya
kashe fitilar ya yi gadon da ita. Ya kwanta tana
manne a jikinsa, jikinta sai bari yake yi na
tsoratar da ta yi.
Zuciyar Haidar fes yau ga shi manne da jawahir
dinsa, abar sonsa shi kuwa ya taba jin jiki me
taushi da santsi kamar na jawahir dinsa? Shi dai
bai gushe ba yana sambatu da jin dadin tattausar
jiki har bacci ya kwashe shi.
Da asuba ya riga ta tashi sai da ya dauko alwala
sannan ya tashe ta ta tafi yo alwala kafin ta
dawo ya tayar da raka’atainil fajri ita ma ta tayar
suna idarwa suka tayar da sallar asuba Haidar ya
ja musu limanci.
Suna idarwa suka ja carbi suka yi ta yin addu’a
har suka shafa ya bude musu kur’ani suka biya
tare suka sake yin addu’a suka shafa.
Ta durkusa gabansa yaya ina kwana. Ya amsa
cikin murmushin jin dadi kin kwana lafiya yaya
tsoro? Ta yi murmushi ta mike ya ce, “Ina za ki?
Sai da ta rissana sannan ta ce, “Kicin za ni. Ya
ce “A’a taho kwanciya za mu yi suka koma gado
suka kwanta.
Bacci ya dade da kwashe su wani gigitaccen bugu
ne ya farkar da su a wahalce Haidar ya zare
jikinsa daga na jawahir ya mike ya nufi kofar ya
bude. Kausar ce ta cukuikuye masa wuyan riga
tana cewa, “Kai wallahi sai ka sake ni takardarta
za ka ba ni ba zan iya zama da miskini ba.
Ya wankawa fuskarta mari ya ce, “Ni kika
shakarwa wuyan riga, dan iska za ki mayar da
ni? An ki a sake ki din ki je ki gayawa duk wanda
za ki gayawa. Ta dafe kunci ni ka mara to
wallahi sai ka gane kurenka. Ta juya ta yi dakinta
ta dauko mayafi ta yi waje ta hau mota ta tuka
kanta ta fice daga gidan.
Kotu ta nufa ta shigar da kara.
Haidar yana gida sun gama shirinsu sun ci
kwalliya kamar masu xuwa fati, sun gama
karyawa ke nan yaron gidansa ya yi sallama a
kofar falon aka amsa masa ba tare da ya shiga
ba ya ce Yallabai ana sallama da kai a waje.
Ya ce, “Okey ga ni nan fitowa.
Ya mike ya fita
Da mamakinsa suka gaisa da bako ba tare da ya
san shi ba. Bako ya mika masa zungureriyar
takarda, “Ni yaron alkali ne ga shi wannan
sammaci ne daga kotu matarka tana kararka.
Haidar ya rinka juya takarda a hannunsa cikin
mamaki ya ce, “Okey je ka na gani. Yaron alkali
ya juya ya tafi, Haidar ya shiga gida
Ya cewa jawahir zai je gida yanzu Abbansa yana
son ganinsa. Ta yi masa kyakkyawar addu’a tare
da fatan Allah ya dawo da shi lafiya.”
A hankali ya rinka juya motar yana mamakin hali
irin na kausar. Yana isa gida ya samu Abbansa a
falo da Anti suka gaisa sai ya mikawa Abbansa
takardar da aka kawo masa ya ware takardar ya
karanta. Abba ya hangame baki tare da yin
salati. Cikin yaya? Me ya hada ku? Haidar ya
kwashe labarin komai ya gaya masa. Abba ya
kama salati amma wannan yarinya ta ci mana
mutunci. Anti ta ce ka sake ta kawai ba sai an je
gaban kotu ta tsinka mu ba.
Nan take Haidar ya rubuta mata takardar saki
daya Anti ta karba ta bawa me aikinta tace ta yi
sauri ta je direba ya kai ta gidan Saddika kawar
Kausar su kaiwa Kausar din.
Kausar kuwa tana ganin takarda ta cika da farin
[Advertisements⬇️]
[Continue Reading⬇️]
ciki inda a nan take ta yi wa alkalin waya ta ce
ta janye shari’ar ta yi sauri ta koma gidan Haidar
daman ta sa ‘yan matanta sun hada mata
kayanta na sawa da duk wani abu na amfaninta
na kwalliya suka judo mata akwatunanta suka
loda su a but direba ya je su zuwa Airport suka
yanki tikiti suka nufi Abuja.
Abbab Haidar ya dube shi ya ce, “Bana so ka sa
damuwa a ranka bare ka zo abin yana damunka
daman na gama shirya muku tafiya xuwa kasar
waje Kai da
jawahir za ku je asibitin Cairo sabo da haka ku je
ku fara shiri nan da sati daya za ku tafi.
“To Abba mun gode Allah ya saka da alheri
Ubangiji ya kara budi.
Haidar ya koma gida yake gayawa jawahir abin
da ya faru duk da jawahir ba ta son zaman
Kausar a gidan amma ba ta ji dadin sakin da
Haidar ya yi mata ba. Ba su da wani lokaci sai
na shiri da ziyartar ‘yan uwa suna yi musu
sallama.
Ranar da suka je Abuja gidan Ankul Anti Maryam
ta ce ya dai ‘yata in ce ko dai har yanzu kina
shan abubuwan da na gaya miki?
“Ai Anti tun ranar da na bar gidan nan ban yi
fashin shan kayayyakin nan ba, don wasu
abubuwan ma idan na hada har da Yayan muke
sha ba tare da ya san ko meye ba.
“Yauwa diyata na sara miki yanzu na san kin
tsumu kin cika da ni’ima sosai karyar Haidar ya
dandana ki ya kuma kusantar wata matar.
“Allah Auntyna, “Suka tafa. Aunty maryam ta
kwaso mata wasu hadin da ta kuma yi tare da
wani turare na gama da ake yi kafin saduwa da
miji, tsaraba dai sosai ta hada mata don tafiya
Cairo.
Sun je gidan Inna gidan Yagwalgwal, gidan Faruk,
gidansu Bilkisu, gidan Abba, gidan Dady, duk
gidan dangi da ‘yan uwa babu inda ba su ziyarta
ba.
Sha biyu na dare jirginsu ya tashi xuwa kasar
Egypt wato inda za su sauka a birnin Cairo inda
asibitin da za a duba Haidar yake.
Ranar da suka dira gajiya ba ta bar su ba
ramuwar bacci suka yi sai washegari suka isa
asibitin. Aka saka Haidar a computer cikin lokaci
kankani suka gano matsalar ba tare da bata
lokaci ba suka yi masa aiki suka kwantar da shi a
asibitin tsawon sati daya saboda magungunan da
yake sha.
Cikin ikon Allah Haidar ya ware ya samu sauki
kamar ba shi ba. Asibitin sun sallame shi sun
dawo Hotel din da suka sauka. Yana kwance a
kan kafet jawahir tana masa tausa sannu a
hankali yana wash! Wash!! Tare da lumshe ido.
Yau duk ya wani shagwabe mata ya narke mata
ta hana ta sukuni daga ya ce, nan yana cuwo sai
ya ce can. Sai bin sa take da lallama cikin
tausayawa da kyar ta samu ya yi bacci ta shiga
tolet ta yi wanka ta fito ta gyara jikinta da
hadadden mayuka masu kamshi tare da turarukan
da ta mulke jikinta kowacce gaba ta jikinta
kamshi take fitarwa.
Ta saka ‘yar bingilar rigar bacci iya cinya me
hannun shimi ta dada feshe dakin da Air
freeshner. Dakin ya dau sanyi da daddadan
kamshi ta haye gado ta shiga bargo ba ta jima ba
bacci ya yi awon gaba da ita.
Haidar da idonsa yake a kanne yana kallonta ya
mike shi ma ya shiga tolet ya watsa ruwa ya fito
ya gama shirinsa ya hade jikinsa da kamshin
turare, ya kashe fitila ya hau gadon ya kunna dim
night dakin ya yi shiru ba ka jin motsin komai sai
karar A.C Haidar ya manne ta a kirjinsa ya matse
ta gam, ya tura harshensa cikin bakinta ya rinka
tsotsa yana wani salo na daban. Da ya gangaro
zuwa kirjinta yayin da ya zare karamar rigar da
take jikinta.
Bayyanar na shanunta a waje shi ya kara gigitar
da shi jikinsa ya hau bari da rawa ya gigice ya 33
dimauce har ya manta a wacce duniyar yake.
[Advertisements⬇️]
[Continue Reading⬇️]