[Advertisements⬇️]
[Continue Reading⬇️]
SALON SO CHAPTER 10
Haidar da jawahir suna zaune a falo suna kallo
jawahir ta kama hamma Haidar ya jawo ta jikinsa
yana shafata ba dai bacci za ki yi ba ki bar ni.?”
Ta daga kai ka san ni da baccin wuri bari na je
daki na kwanta, “Ya langabe murya gaskiya ba za
ki tafi ki bar ni tun yanzu ba.”
Ya rungume ta ya gyara mata kwanciya a jikinsa
yana shafa kanta yi bacci a haka in na gama
kallo na kai ki dakinki. Cikin mintina kadan bacci
ya kwashe jawahir dadi ya cika zuciyar Haidar jin
jawahir rungume a jikinsa taushin fatarta da
kamshin jikinta shi suke dada sa shi nishadi.
Kausar ta yi sallama ta shigo falon ba dan sanin
muhimmancin sallama a addinin musulunci ba da
bai amsa mata ba. Ya dako kai ya kalle ta, “Ina
kika je sai yanzu da daddaren nan za ki dawo
bayan na ce ki dawo da wuri.?”
Ta kalle shi ta ja tsaki, “To ina ruwanka da
dawowata da wuri ko ba da wuri ba? Kai ba wani
cikakken namiji ba bare ka ce za ka yi kishina.”
Jawahir ta dan motsa ya sake rungume ta yana
jijjigata kamar yarinyar goye. Kausar ta yi tsaki
an dai fadi ba nauyi miskinin kawai kana
luguiguita yarinya kai ba wani katabus za ka iya
yi mata ba.” Ta shige dakinta Haidar kuwa ya yi
mata shiru ne gudun kada jawahir ta farka amma
ya ji haushin maganar da ta yaba masa. Da ya ji
kallon ma ya ginshe shi ba zai iya ci gaba da
kallon ba, don tsananin dacin da zuciyarsa take yi
Jawahir da tun shigowar Kausar ta farka ta ji duk
abin da kausar ta gayawa Haidar ranta ya yi
mugun baci, ba ta san sanda hawaye ya fara
zubo mata ba. Haidar da ya yunkura zai mike da
jawahir a kafadarsa sai ya kula hawayen da take
yi hankalinsa ya sake tashi ya kira sunanta,
“Jawahir lafiya?”
Tayi saurin zamewa daga jikinsa ta durkusa kasa
tana kuka ta fara rokonsa don Allah don Annabi
yaya ka yi hakuri ka yafe min abin da na yi maka,
ni na jawo maka matsalar da kake ciki wallahi
tallahi ba da niyya na yi maka haka ba kan
[Advertisements⬇️]
[Continue Reading⬇️]
tsautsayi ne da kaddara, ina neman afuwarka da
gafararka ko na samu sassauci a zuciyata.”
Ya mike tsaye ya kamo kafadunta ya dago ta ya
rungume ta a jikinsa yana share mata hawayen,
“Yi shiru babyna daina kuka ba so ki kuma irin
wannan tunanin a zuciyarki, ki sani duk abin da
Allah ya yi zai samu bawa daman tun fil’azal
rubutacce ne, kuma babu wanda ya isa ya
kankare shi ko ya goge shi. Don haka ki kaddara
daman can Allah ya yi hakan za ta faru da ni, don
haka ni ba na so na ji kina cewa ke ce sanadi
kada ki kuma fada, ni na yarda da kaddara don
haka ba na zarginki da komai, ki kwantar da
hankalinki ba na son ganin ki cikin damuwa, kin ji
ko. Ta daga kai alamar amsawa, “To mu je ki
kwanta. Yana rugume da ita har dakinta, ya raka
ta tolet ta yi borush ya riko ta sai da ya kwantar
da ita a gadonta ya ja bargo ya rufe ta ya kunna
mata A.C ya sumbace ta a kumatu ki yi bacci
lafiya babyna. Ya juya ya fita ya nufi nasa dakin.
Yana fita jawahir ta mike ta dauko tsaleliyar rigar
baccinta ta saka ta shafe jikinta da humra. Ta
dade feshe dakin da Air Freeshner nan da nan
sanyin A.C da daddadan kamshi suka shiga tashi.
Ta matsa mouth freeshner a bakinta nan da nan
sanyayyen kamshi ya rinka fita ta haye gadonta
ta yi lumtsim da ita.
Haidar ya shigo wanka ya fito ya shafe jikinsa da
turare ya hau gado dan kwanciya amma ina
baccin ya gagara sai juyi yake yi yana tunano
lallausan jikin jawahir da taushinsa, ya san ina
bacci zai dauke shi, ya sa kayan baccinsa ya fito
ya rufe dakinsa ya nufi dakin jawahir.
Ya sa safayar mukullinsa ya bude dakin ya shiga
ya mayar ya rufe. Ya shiga cikin dakin nata
wanda sanyin A.C ya gama ratsa shi, ga man
nan na turarenta mai dadin kamshi yana tashi.
Ya kunna fitila ya yaye bargon da ta rufa ya kalle
ta cikin tsaleliyar rigar baccinta wadda ta kara
fito mata da sigar kyanta, baccinta take yi hankali
kwance.28/32
[Advertisements⬇️]
[Continue Reading⬇️]